Labarai
Kotu ta nemi yansanda su biya matan da suka tilasta wa tube hijabi dala miliyan 17
Rundunar ‘yan sandan birnin New York za ta biya dala miliyan 17.5, a wani shari’ar da wasu mata Musulmi suka jagoranta, waɗanda aka tilasta musu cire hijabi yayin da aka ɗauki hotonsu.
Shari’ar ta 2018 ta bayar da hujjar cewa Jamilla Clark da Arwa Aziz sun fuskanci cin zarafi na ‘yancin yin addini da kuma ta rayuwa.
Lauyoyi sun ce sama da mutum 3,600 ne suka cancanci a biya su karkashin yarjejeniyar.
Ƴan sanda sun canza tsari shekaru huɗu da suka gabata don ba da izinin sanya hijabi.
Birnin ya ce lamarin ya haifar da sauyi mai kyau.
Dole ne alkali na tarayya da ke sa ido kan shari’ar ya amince da yarjejeniyar biyan diyyar.
Kamar yadda bayanan kotun suka nuna, Ms Clark ta yi kuka tare da rokon a bar ta saka hijabinta yayin da ‘yan sanda suka ɗauki hotonta.
“Lokacin da suka tilasta min cire hijabi na, sai na ji kamar tsirara nake, bani da tabbacin ko kalmomi za su iya kwatanta yadda nake ji da kuma cin zarafina da aka yi,” in ji Ms Clark a wata sanarwa a ranar Juma’a.
-
Fasaha6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Da Kamfanin Sarrafa Sinadarin Batira a Lafiya
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Labarai1 day ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai6 days ago
Mbappe ya sanar da cewa zai bar PSG a karshen kaka
-
Fasaha3 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai3 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai3 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana