Connect with us

Ilimi

Maniyyata 51,447 Ne Za Su Sauke Farali A Aikin Hajjin Bana – NAHCON

Published

on

Hukumar Alhazai ta Najeriya, ta ce aƙalla maniyyatan Najeriya 51,447 ne za su sauke farali a aikin Hajjin bana a ƙasar Saudiyya.

Shugaban hukumar, Malam Jalal Arabi, ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai da aka gudanar ranar Juma’a a Abuja.

Arabi ya ce hukumar na tsare-tsare wajen ganin ta gudanar da aikin Hajji cikin nasara, ko da kuwa za a fuskanci kalubale.

Ya nanata cewa Msulman Najeriya za su yi aikin Hajjin 2024 a adadin da babu wanda ya taɓa tunani.

“Shirye-shiryen Hajjin bana na ɗaya daga cikin mafi wahala da aka taɓa gani,” in ji shi.

Ya ce a baya, an samu lokaci mai yawa na yin shirin da ya kamata, amma a wannan karon, Saudiyya ba ta ba su isasshen lokaci ba.

Malam Arabi ya ce gwamnatin tarayya ta shiga taimaka ta hanyoyi da dama, musamman ma ɓullo da wasu tsare-tsare na tallafa wa hukumar domin tabbatar da cewa al’amura su tafi yadda ya dace.

Ma’aikatar aikin Hajji da Umrah ta Saudiyya ta ware wa Najeriya kujeru 95,000 domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2024.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai11 hours ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai13 hours ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai14 hours ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi14 hours ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai1 day ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai2 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai2 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai2 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai2 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara