Labarai
Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Yi Rijista a Jam’iyyar APC
Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Malam Mani Malam Mummuni, ya yi rijista a hukumance a matsayin cikakken ɗan jam’iyyar APC.
An gudanar da rajistar ne a Fadar Gwamnatin Jihar Zamfara da ke Gusau, jim kaɗan bayan kaddamar da wani taron horaswa na kwanaki biyu kan rijistar ’yan jam’iyya a dukkanin ƙananan hukumomi 14 da kuma gundumomi na jihar.
Da yake jawabi a wajen taron, Mataimakin Gwamnan ya ce muhimmancin wannan horo ba zai misaltu ba.
A cewarsa, an zaɓi mahalarta taron ne da kulawa domin su zama masu horaswa da kuma masu jagorantar aikin rijistar ’yan jam’iyya a ƙananan hukumominsu da gundumominsu.
“Kamar yadda kowa ya sani, jam’iyyarmu na ci gaba da karɓar sababbin mambobi da dama a faɗin jihar. Don haka yana da matuƙar muhimmanci tsarin rijistar ’yan jam’iyya ya kasance mai tsari, gaskiya da kuma kulawa ta yadda ya dace,” in ji shi.
Malam Mani ya yabawa Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, kan ƙoƙarinsa na ci gaba da bunƙasa jam’iyyar.
Ya kuma jaddada cewa yayin da ƙarin jama’a ke ci gaba da rungumar manufofin jam’iyyar tare da shiga cikinta, ya zama dole a samar da ingantaccen kundin rajistar mambobi wanda zai nuna ainihin ƙarfin magoya bayan jam’iyyar tun daga matakin ƙasa.
Mataimakin Gwamnan ya buƙaci mahalarta taron su ɗauki wannan aiki da muhimmanci, yana mai cewa nasarar shirin zai dogara ne kan jajircewarsu, gaskiya da kuma sadaukarwarsu.
Mani Malam Mummuni ya ƙara da cewa wannan shiri ba wai don yin rijistar ’yan jam’iyya kaɗai ba ne, har ma don ƙarfafa tsarin jam’iyyar a matakin ƙasa da kuma gina hadaddiyar dandali da zai ci gaba da wakiltar muradu da burin al’ummar Jihar Zamfara.
Haka kuma, a madadin Gwamnan Jihar, Dakta Dauda Lawal, Mataimakin Gwamnan ya yi wa mahalarta taron fatan samun muhawara mai amfani da kuma nasarar gudanar da taron.
Mataimakin Gwamnan ya yi rijistar ne tare da wasu mambobin Majalisar Zartarwa ta Jihar.
COV / AMINU DALHATU
-
Labarai7 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Labarai7 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai4 days agoRanar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata
-
Labarai7 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
-
Labarai7 days agoRamadan: Tinubu Ya Kara Jaddada Kudirinsa na Inganta Rayuwar Jami’an Soji
-
Labarai4 days agoGwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya
-
Labarai7 days agoTsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki
-
Labarai4 days agoSojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina
