Connect with us

Labarai

Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Yi Rijista a Jam’iyyar APC

Published

on

Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Malam Mani Malam Mummuni, ya yi rijista a hukumance a matsayin cikakken ɗan jam’iyyar APC.

An gudanar da rajistar ne a Fadar Gwamnatin Jihar Zamfara da ke Gusau, jim kaɗan bayan kaddamar da wani taron horaswa na kwanaki biyu kan rijistar ’yan jam’iyya a dukkanin ƙananan hukumomi 14 da kuma gundumomi na jihar.

Da yake jawabi a wajen taron, Mataimakin Gwamnan ya ce muhimmancin wannan horo ba zai misaltu ba.

A cewarsa, an zaɓi mahalarta taron ne da kulawa domin su zama masu horaswa da kuma masu jagorantar aikin rijistar ’yan jam’iyya a ƙananan hukumominsu da gundumominsu.

“Kamar yadda kowa ya sani, jam’iyyarmu na ci gaba da karɓar sababbin mambobi da dama a faɗin jihar. Don haka yana da matuƙar muhimmanci tsarin rijistar ’yan jam’iyya ya kasance mai tsari, gaskiya da kuma kulawa ta yadda ya dace,” in ji shi.

Malam Mani ya yabawa Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, kan ƙoƙarinsa na ci gaba da bunƙasa jam’iyyar.

Ya kuma jaddada cewa yayin da ƙarin jama’a ke ci gaba da rungumar manufofin jam’iyyar tare da shiga cikinta, ya zama dole a samar da ingantaccen kundin rajistar mambobi wanda zai nuna ainihin ƙarfin magoya bayan jam’iyyar tun daga matakin ƙasa.

Mataimakin Gwamnan ya buƙaci mahalarta taron su ɗauki wannan aiki da muhimmanci, yana mai cewa nasarar shirin zai dogara ne kan jajircewarsu, gaskiya da kuma sadaukarwarsu.

Mani Malam Mummuni ya ƙara da cewa wannan shiri ba wai don yin rijistar ’yan jam’iyya kaɗai ba ne, har ma don ƙarfafa tsarin jam’iyyar a matakin ƙasa da kuma gina hadaddiyar dandali da zai ci gaba da wakiltar muradu da burin al’ummar Jihar Zamfara.

Haka kuma, a madadin Gwamnan Jihar, Dakta Dauda Lawal, Mataimakin Gwamnan ya yi wa mahalarta taron fatan samun muhawara mai amfani da kuma nasarar gudanar da taron.

Mataimakin Gwamnan ya yi rijistar ne tare da wasu mambobin Majalisar Zartarwa ta Jihar.

COV / AMINU DALHATU

Labarai

Labarai3 hours ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Labarai3 hours ago

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara

Hukumar Kwastam ta Najeriya, reshen Jihar Kwara, ta ce ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta da kuma...

Labarai3 hours ago

Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Yi Rijista a Jam’iyyar APC

Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Malam Mani Malam Mummuni, ya yi rijista a hukumance a matsayin cikakken ɗan jam’iyyar APC. An...

Labarai3 hours ago

Jami’ar Bayero Kano Ta Yi Martani Kan Zargin Damfarar Dalibi

Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta yi martani kan zarge-zargen da ke yawo cewa wani mutum da ake zargin yana ikirarin...

Labarai3 hours ago

Matashi Mai Digiri Na Farko Na Sayar Da Ruwan Leda A Taraba

Wani matashi mai digirin na 2 a fannin Ilimin (Theology) kuma wanda ya kammala karatun Physics, mai suna Hilekann Eric,...

Labarai2 days ago

Tinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa

Daga Bello Wakili Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Lamido Abubakar Yuguda a matsayin Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa CBN,...

Labarai2 days ago

An Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau

Daga Aminu Dalhatu Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Kabir Yahaya Gusau a matsayin Darakta Janar na...

Labarai2 days ago

Kwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u  Hukumar Kwastam ta Kasa reshen Jihar Kwara ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta...

Labarai3 days ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai4 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Mafi Shahara