Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Raba Tallafi Ga Wadanda ‘Yan Fashin Daji Suka Raba Da Gidajen su

Published

on

Gwamnatin jihar Kaduna ta fara rabon kayan abinci ga ‘yan gudun hijira sama da dubu daya da ‘yan fashi daji suka raba da gidajensu a karamar hukumar Kajuru.

 

Mataimakiyar gwamnan jihar, Dakta Hadiza Balarabe da ta kaddamar da rabon kayayyakin a karamar hukumar Kajuru ta ce gwamnati ta kudiri aniyar samar da yanayi mai aminci da wadata ga kowa da kowa kuma ba za ta huta ba har sai an kawar da barazanar ‘yan fashin daji.

 

Dokta Balarabe wanda mataimakin shugaban ma’aikata a ofishinta, Mista James Kanyip ya wakilta, ya bayyana cewa, a matsayinsu na gwamnati, ya zama wajibi su tabbatar da tabbatar da walwala da jin dadin al’ummarta, musamman a wannan lokaci da suke cikin mawuyacin hali.

 

Ta ce Gwamna Uba Sani ya fahimci radadin da suke ciki sakamakon rashin tausayi da Imani da aka nuna musu don haka ba a za ayi kasa a gwiwa ba wajen basu taimako da tallafi ga wadanda abin ya shafa.

 

A cewar Dokta Balarabe, kayayyakin tallafin da aka raba sun hada da manyan motoci guda biyu da garin masara da kuma shinkafa.

 

Da yake jawabi ga ‘yan gudun hijirar, Sakataren zartarwa na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Kaduna KADSEMA, Dokta Usman Mazadun ya ce kimanin ‘yan gudun hijira dubu dari biyu da casa’in ne aka samu a kananan hukumomi 12 na jihar Kaduna.

 

Mista Mazadun ya bayyana cewa a karamar hukumar Chikun, matsalar rashin tsaro ta shafi al’ummomi 134 da kuma mutane 26,345 da suka rasa matsugunansu yayin da a Birnin Gwari, al’ummomi 84 da abin ya shafa kuma 70,893 suka rasa matsugunansu.

 

Dakta Usman Mazadun ya kuma bayyana cewa nan da ‘yan makonni masu zuwa gwamnati za ta mika rabon tallafin ga daukacin al’ummomin da abin ya shafa a kananan hukumomi 12 da aka tantance.

 

Da yake magana da manema labarai, shugaban karamar hukumar Kajuru, Mista Ibrahim Gajere, ya bayyana fatansa cewa, ‘yan gudun hijira na karamar hukumar Kajuru ne suka fara cin gajiyar tallafin.

 

A nasa jawabin, Basaraken Kufana Gwan Kufana, Mista Titus Dauda, ​​ya nuna matukar godiya ga Gwamnan, da kuma tawagarsa bisa namijin kokarin da suke yi na ganin an kai agaji ga wadanda suka fi bukata.

 

Ya bayyana cewa aikin alheri ba wai kawai samar da ababen more rayuwa ba ne, har ma ya kara dankon zumunci tsakanin gwamnati da jama’a.

 

 

Wadanda suka ci gajiyar tallafin, sun nuna jin dadinsu ga jihar Kaduna bisa samar da tallafin da suka hada da Shinkafa da garin tuwa.

 

Aminu Dalhatu/Wababe

Labarai

Labarai19 hours ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai20 hours ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai21 hours ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi22 hours ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai2 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai2 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai3 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai3 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai3 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara