Connect with us

Labarai

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Published

on

Daga Abdullahi Jalaluddeen

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar.

Zaɓen, wanda aka gudanar a ranar Talata, ya fitar da Umar Haruna Doguwa a matsayin sabon Shugaban Jam’iyyar na Jiha.

Doguwa ya ajiye muƙaminsa na Kwamishinan Albarkatun Ruwa na Jihar Kano domin tsayawa takarar shugabancin jam’iyyar.

Salisu Maje Ahmad Gwangwazo ya zama Mataimakin Shugaban Jiha, yayin da Farfesa Yusuf Muhammad Sabo Bichi aka zaɓe shi a matsayin Sakataren jam’iyyar na jiha.

Haka kuma, an zaɓi Abdul Adamu Fagge a matsayin Mai Ba da Shawara kan Harkokin Shari’a, tare da Bashir Yusuf Tudun Wuzirci a matsayin Mataimakin Mai Ba da Shawara kan Shari’a.

Kabiru Sule Rogo ya samu muƙamin Ma’aji, yayin da Umar Yusuf Umar ya zama Mataimakin Ma’aaji. An kuma zabi Ma’aruf Abdullahi Garo a matsayin Sakataren Kuɗi, sai kuma Mustafa Muhammad Kalwa a matsayin Mataimakin Sakataren Kuɗi.

Hakazalika,  Dakta Kabiru Hussaini Zawaciki ya zama Sakataren Tsare-tsare, tare da Abdussalam Umar a matsayin mataimakinsa.

Auwalu Abdullahi ya zama Sakataren Yaɗa Labarai, wanda Sani Fata zai taimaka masa a matsayin mataimaki.

Yayin da Bashir Mai Sango ya zama Sakataren Jin Daɗin Mambobi, tare da Garba Hussaini a matsayin mataimaki. Abubakar Salisu zai riƙe muƙamin Mai Binciken Kuɗi, yayin da Nura Muhammad ya zama Mataimakin Mai Binciken Kuɗi.

Labarai

Labarai2 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi2 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai3 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai4 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai1 day ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai2 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara