Connect with us

Labarai

Jam’iyyar APC Ta Zargi Tsohon Gwamna Tambuwal da Yin Sakaci da Ƙaramar Hukumar Sa

Published

on

Jam’iyyar APC a Jihar Sakkwato ta zargi tsohon Gwamnan jihar, Alhaji Aminu Waziri Tambuwal, da rashin yin abin da ya dace ga Ƙaramar Hukumar Tambuwal a lokacin da yake kan mulki.

Shugaban Jam’iyyar APC na Jihar Sakkwato, Isah Sadiq Acida, ne ya yi wannan zargi a wani taro da Dandalin Tuntuɓa, Wayar da Kai da Tattara Magoya bayan APC na Tambuwal ya shirya.

Rahoton Rediyo Nijeriya a Sakkwato ya bayyana cewa wannan zargi ya biyo bayan gabatar da rahoton da Kwamitin Bincike na Jihar Sakkwato ya kafa kan mulkin tsohon Gwamna Aminu Waziri Tambuwal na jam’iyyar PDP, inda aka kuma zarge shi da almundahana da kuɗaɗen gwamnati da suka haura naira biliyan ɗari da goma sha bakwai (₦117bn) a lokacin mulkinsa.

Shugaban jam’iyyar ya ce APC a Jihar Sakkwato ta samu gagarumar nasara a Ƙaramar Hukumar Tambuwal, sakamakon sauya sheƙar da kansiloli uku, tsohon mataimakin shugaban ƙaramar hukuma, da kuma wasu manyan jagororin jam’iyyar PDP suka yi zuwa APC mai mulki. Haka kuma, an ba jam’iyyar gudunmawar kuɗi har naira miliyan goma (₦10m) domin ƙarfafa ayyukan wayar da kai da tattara magoya baya.

Da yake jawabi ga mahalarta taron, Mataimakin Shugaban Dandalin, Faruk Dayyabu, ya ce an shirya taron ne domin, a tsakanin sauran manufofi, cin gajiyar yalwar basirar da Allah ya bai wa matasa da al’ummar Ƙaramar Hukumar Tambuwal.

NASIR MALALI

Labarai

Labarai6 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara