Connect with us

Labarai

Tsaftar Muhalli: An Bukaci Shugabannin Su Yi Koyi da Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

An bayyana rashin tsaftar muhalli a matsayin babbar hanyar haddasa matsalolin lafiya a cikin al’umma.

Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu, Dokta Builder Muhammad Uba, ya bayyana hakan a yayin aikin tsaftar muhalli na kowane wata da aka gudanar a Birnin Kudu.

Shugaban ya sake jaddada jajircewarsa wajen tabbatar da tsaftar muhalli ta hanyar halartar aikin tsaftar muhalli na karshen wata, wanda ake gudanarwa a duk ranar Asabar ta karshe ta kowane wata.

Dokta Muhammad Uba, ya jaddada muhimmancin tsaftar muhalli tare da kira ga al’ummar yankin da su rika tsaftace muhallinsu a kowane lokaci.

Ya bayyana cewa kula da tsaftar muhalli hakki ne da ya rataya a wuyan kowa da kowa domin samar da muhalli mai tsafta da lafiya.

Haka kuma, ya tabbatar wa al’umma cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da ba da goyon baya ga shirye-shiryen da ke inganta tsaftar muhalli da kula da lafiyar jama’a.

Builder ya kuma bukaci mazauna yankin da su dauki alhakin kula da muhallinsu tare da yin aiki tukuru domin tsaftace Karamar Hukumar ta Birnin Kudu.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa an gudanar da atisayen tsaftar muhalli na kowane wata a wuraren taruwar jama’a, kasuwanni da unguwanni, inda mahalarta suka bukaci masu ruwa da tsaki su yi koyi da kyakkyawan jagorancin Shugaban Karamar Hukumar tare da ba da fifiko ga tsaftar muhalli.

 

Labarai

Labarai3 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai23 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara