Connect with us

Labarai

Baragurbi a Aikin Jarida na Barazana ga Sahihancin Kafafen Yada Labarai – Shugaban NUJ-FRCN

Published

on

Shugaban Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Najeriya (NUJ), reshen FRCN Kaduna, Kwamared Umar Adamu Sarkinfada, ya bayyana cewa mummunan aikin jarida na zama babbar barazana ga ƙwarewa da amincewar jama’a da kuma zaman lafiyar ƙasa.

A cikin sakon sabuwar shekara da ya aikewa ’yan jarida, Sarkinfada ya gargaɗi cewa yaɗa labaran ƙarya da rashin kwaklwaran binciken jarida da kuma ayyukan mutanen da ba su da horo amma suke kiran kansu ’yan jarida, na lalata martabar aikin jarida tare da raunana ayyukan sahihan ’yan jarida.

Ya bayyana cewa rahotannin da ba a tantance ba kuma masu tayar da hankali, musamman kan muhimman batutuwan ƙasa, na iya haddasa firgici, yaɗa bayanan ƙarya da kuma tashin hankalin al’umma, yayin da ayyukan marasa ƙwarewa ke bata sunan ’yan jarida masu bin ka’ida.

Shugaban NUJ ya yi kira ga ’yan jarida da su sake tsayawa tsayin daka kan ɗabi’un aikin jarida, yana jaddada muhimmancin sahihanci, daidaito, tantance gaskiya da yin cikakken bincike bisa manufofin NUJ da ƙa’idar aiki.

Ya kuma yi kira ga kafafen yaɗa labarai da su ƙarfafa hanyoyin sa-ido na cikin gida tare da bada horo na ci gaba mai muhimmanci, yayin da ya shawarci jama’a da su yi dogara ga sahihan hanyoyin labarai tare da tantance bayanai kafin su yaɗa su.

Sarkinfada ya sake jaddada kudurin reshen NUJ FRCN Kaduna na inganta ƙwarewa da mutuncin kafafen yaɗa labarai, yana bayyana sabuwar shekarar a matsayin wata dama ta sabunta jajircewa ga aikin jarida mai inganci a Najeriya.

 

Labarai

Labarai17 hours ago

Tinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa

Daga Bello Wakili Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Lamido Abubakar Yuguda a matsayin Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa CBN,...

Labarai18 hours ago

An Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau

Daga Aminu Dalhatu Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Kabir Yahaya Gusau a matsayin Darakta Janar na...

Labarai18 hours ago

Kwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u  Hukumar Kwastam ta Kasa reshen Jihar Kwara ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta...

Labarai2 days ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai3 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi3 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai3 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai3 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Mafi Shahara