Connect with us

Labarai

Gwamna Nasarawa Ya Ce Za Su Samar da Masana’antu Don Ayyukan Yi

Published

on

Gwamnan Jihar Nasarawa, Injiniya Abdullahi Sule, ya bayyana cewa hangen nesansa na ƙarfafa masana’antu a jihar shi ne domin ƙirƙirar ayyukan yi da kuma inganta rayuwar jama’ar jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne a Fadar Gwamnati ta Lafia, yayin da yake karɓar bakuncin sabbin shugabannin Ƙungiyar ‘Yan Jarida Masu aiko rahotann dake Jihar (Correspondents’ Chapel).

Ya ce baya ga jawo ‘yan kasuwa masu saka jari a fannin masana’antu da ma’adinai, gwamnatin sa tana kuma zuba jari mai yawa a harkar noma.

“Ɗaya daga cikin abubuwan da ke ba ni farin ciki shi ne harkar noman shinkafa. Ka san muna da wata ƙaramar gona mai girman hektare 3,300 domin noman shinkafa.

Ina alfahari da gonar shinkafar mu domin mun fara girbi, kuma dukkan alamu sun nuna cewa amfanin gona a wannan kakar ya fi na bara, musamman a yawan amfanin da ake samu a kowace hekta,” in ji shi.

Gwamna Sule ya ce yana da cikakkiyar niyya ta ƙaddamar da aikace-aikace da shirye-shirye da za su tabbatar da amfanin kai tsaye ga jama’ar jihar.

A cewarsa, ɗaya daga cikin dalilan da ke haifar da kalubale da rashin tsaro a arewacin ƙasar, shi ne mutane da yawa ba su da abin yi.

“Ka san wannan shi ne ɗaya daga cikin abubuwan da ke jawo matsalar tsaro.

A da, lokacin da muke yara, akwai masana’antar yadi (textile) a Kaduna da ƙananan masana’antu a sassa daban-daban na arewa, mutane suna da abin yi.

Ba a cika jin labarin rashin tsaro ba, domin mutane suna zuwa gona, suna yin aikinsu da halaltattun hanyoyi,” in ji gwamnan.

Yayin da yake taya sabbin shugabannin ƙungiyar ‘yan jarida murna bisa nasarar rantsar da su, Gwamna Sule ya kuma bukace su su tsaya kan ƙa’idar aikin jarida ta gaskiya da adalci.

A nasa jawabin, Shugaban Ƙungiyar ‘Yan Jarida na Jihar Nasarawa, Alhaji Abubakar Abdullahi, ya ce ziyarar ta kasance ne domin gabatar da sabbin shugabanni ga gwamna da kuma ƙarfafa dangantaka tsakanin gwamnati da ‘yan jarida.

Ya yaba wa Gwamna Sule bisa aikace-aikacen ci gaba da gwamnatin sa ke aiwatarwa, musamman gona mai girman hekta 3,300 a Jangwa, karamar hukumar Awe, wadda amfanin shinkafar ta za ta shiga kasuwa a ƙarƙashin sunan alamar jihar “NASACCO Rice.”

Ya kuma ambaci wasu muhimman ayyuka da suka haɗa da gine-ginen gadar sama da ƙasa a Lafia, ayyukan gadar Keffi/Akwanga, sabuwar cibiyar ma’aikata ta jihar, da kuma biyan fansho da hakkokin ma’aikata a kan lokaci.

“Gwamnatinka tana ci gaba da nuna goyon baya ga ci gaban aikin jarida, kuma muna godiya da kyakkyawar dangantaka da muke da ita, tare da fatan za ta ci gaba da dorewa,” in ji shi.

Aliyu Muraki, Lafia.

Labarai

Labarai18 hours ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Labarai18 hours ago

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara

Hukumar Kwastam ta Najeriya, reshen Jihar Kwara, ta ce ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta da kuma...

Labarai18 hours ago

Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Yi Rijista a Jam’iyyar APC

Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Malam Mani Malam Mummuni, ya yi rijista a hukumance a matsayin cikakken ɗan jam’iyyar APC. An...

Labarai18 hours ago

Jami’ar Bayero Kano Ta Yi Martani Kan Zargin Damfarar Dalibi

Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta yi martani kan zarge-zargen da ke yawo cewa wani mutum da ake zargin yana ikirarin...

Labarai18 hours ago

Matashi Mai Digiri Na Farko Na Sayar Da Ruwan Leda A Taraba

Wani matashi mai digirin na 2 a fannin Ilimin (Theology) kuma wanda ya kammala karatun Physics, mai suna Hilekann Eric,...

Labarai2 days ago

Tinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa

Daga Bello Wakili Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Lamido Abubakar Yuguda a matsayin Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa CBN,...

Labarai2 days ago

An Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau

Daga Aminu Dalhatu Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Kabir Yahaya Gusau a matsayin Darakta Janar na...

Labarai2 days ago

Kwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u  Hukumar Kwastam ta Kasa reshen Jihar Kwara ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta...

Labarai3 days ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai4 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Mafi Shahara