Labarai
Matasa Dubu Ɗaya Za Su Samu Horon Fasahar Zamani A Nasarawa — Remi Tinubu
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta bayyana cewa matasa dubu ɗaya (1,000) za su samu horo kan tsaron yanar gizo (cyber security) da fasahar binciken dijital (digital forensics) ta hanyar Cibiyoyin Koyon Fasahar Dijital ƙarƙashin Shirin Renewed Hope Initiative (RHI) a Jihar Nasarawa.
Uwargidan Shugaban Ƙasan ta bayyana haka ne yayin bikin kaddamarwa da miƙa Cibiyar Koyon Fasahar Dijital (Digital Learning Center) a Lafia da wasu jihohin ƙasar.
Sanata Oluremi Tinubu ta ce, shirin horon matasan wanda za a rika gudanarwa a kowane mako daga yanzu har zuwa watan Disamba na shekara mai zuwa, yana da nufin yakki da laifukan yanar gizo (cyber crimes) da kuma ƙarfafa matasa su samu ƙwarewa ta yadda za su dogara da kansu a rayuwa.
Uwargidan Shugaban Ƙasan ta yaba wa Daraktan Hukumar NITDA, Malam Kashifu Inuwa Abdullahi, bisa ƙoƙarin gina cibiyoyi 15 na koyon fasahar dijital tare da haɗin gwiwar Renewed Hope Initiative, domin bunƙasa damar samun ilimi ta fasahar zamani a ƙasar.
A nasa jawabin, Daraktan Janar na NITDA, Malam Kashifu Inuwa Abdullahi, ya bayyana cewa dijitalizashan (digitalization) muhimmin ginshiƙi ne a cikin manufofin sauyin gwamnati ta yanzu, don haka aka kafa cibiyoyi 296 na koyon fasahar dijital a fadin ƙasar.
Ya ƙara da cewa a bana, NITDA tana shirin ƙara cibiyoyi 148, wanda hakan zai kai adadin cibiyoyi zuwa 586 kafin shekarar 2027.
Shi ma Daraktan Janar na Hukumar Fasahar Sadarwa da Tattalin Arzikin Dijital ta Jihar Nasarawa (NASITDA), Sani Haruna Sani, ya bayyana cewa wannan cibiya za ta zama hedikwatar horo kan ilimin dijital, tsaron yanar gizo da kuma binciken forensics a jihar.
Ya yi kira ga matasan jihar da su amfana da wannan dama domin su ƙara kwarewa a fannin fasahar zamani, su taimaka wajen ci gaban tattalin arzikin jihar da ƙasa baki ɗaya.
Aliyu Muraki, Lafia
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
