Ilimi
Gwamnatin Zamfara Ta Koka Game Da Rashin Zuwan Likitoci Aiki A Babban Asibitin Jihar
Gwamnatin jihar Zamfara ta bayyana damuwarta kan yadda likitoci ke kin zuwa aiki musamman a lokutan da suke kai ziyara wuraren kiwon lafiya da ba a shirya ba.
A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na ma’aikatar lafiya ta jihar, Suleiman Isah ya fitar, ya ce kwamishinan lafiya Dr. Nafisa Muhammad Maradun ta yi gargadi ga likitoci a babban asibitin garin Gusau, bayan da suka gano rashin zuwan su a wata ziyarar ba-zata.
Dakta Maradun, wadda ta kai ziyarar bazata asibitin, ta ce ta firgita da ganin cewa babu wani likita da ke bakin aiki, inda ta bayyana hakan a matsayin wani abu da ke faruwa a baya.
Ta yi Allah wadai da lamarin a matsayin abin da ba za a amince da shi ba, ta kuma yi gargadin cewa, duk likitan da ba ya son bin ka’idojin kwararru da na gwamnati, ya kamata ya yi murabus maimakon kawo cikas ga tsarin kiwon lafiyar jihar.
“Idan ba za su iya yin biyayya ba, to su yi murabus, ko kuma su fuskanci sakamako daga gwamnatin jihar,” Kwamishinan ta yi gargadin.
Ta kuma jaddada cewa gwamnatin jihar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen daukar matakan ladabtarwa a kan ma’aikatan lafiya da ke yin kuskure ko wasa da aiki.
Dr Maradun ta jaddada cewa jin dadin marasa lafiya ya kasance babban fifikon gwamnati.
REL/AMINU DALHATU.
-
Labarai4 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai1 day agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai2 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai5 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
