Connect with us

Labarai

Kananan Hukumomi 774 Za Su Amfana Da Tallafin Dangote Na Biliyan 15

Published

on

A wani mataki na rage radadin talauci a tsakanin al’umma, gidauniyyar Dangote ta kaddamar da tallafin rabon abinci na kasa a jihohin kasar nan inda mutane miliyan daya suka amfana.

Alhaji Aliko Dangote ya tabbatar da cewa tallafin zai game dukkanin kananan hukumomin kasar nan 774, na kimanin buhunan shinkafa milyan daya me nauyin kilo 10.

Jihar Kano ta samu kaso mafi girma inda mutane 120,000 suka amfana wanda daga bi sani rabon zai ci gaba a sauran jihohin kasar nan.

Haka zalika rabon shinkafa mai kilo 10 zai ci gaba a dukkanin sauran kananan hukumomi na Jihar Kano.

Bikin kaddamar da rabon abincin dai ya gudana ne a budadden dakin taro na fadar Gwamnatin Kano da shugaban rukunonin kamfanin Dangote Alhaji Aliko Dangote ya samu halarta da kuma Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf.

A cewar Alhaji Aliko Dangote , sun ga dacewar raba kayan abincin ne ba wai kawai don magance matsalar yunwa ba, har da batun saukakawa al’umma wajen gudanar da rayuwa a kasa ba-ki daya.

“Hakan kuwa ya zama wajibi duba da muhimmancin zumunci da ‘yan uwan taka dake tsakanin mu, da kuma hadin kai a wannan lokaci da ake fusakantar kalubalen rayuwa.

“A wannan wata na Ramadan, lokaci ne da muke sadar da halayen nagarta, wanda ke taimakawa wajen tallafawa al’umma”.

“Ina da kwarin gwuiwar sanar daku cewa wannan tallafin na yanzu na musamman ne, duk da cewar mun yi irin sa a kasa da wata guda da ya gabata, amman muka ga dacewar sake tallafawa al’umma musamman a wannan lokaci na Azumin watan Ramadan.

Attajirin Alhaji Aliko Dangote, ya shaidawa gangamin taron al’ummar cewa wannan kari ne akan tallafin da ya gudana na mutane dubu goma da ake ciyarwa kullum a Jihar Kano, yace Tallafin shinksfar Mai kilo goma da ya kaddamar kimanin miliyan Daya wanda ya lakume kudade Naira bilyan 15 a kasa ba-ki daya.

Da yake jawabi Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya yabawa shirin rabon tallafin kayan abincin inda yace yazo a dai-dai lokacin da dimbin al’umma ke bukatar hakan.

Gwamnan ya bukaci kwamitin da aka dorawa nauyin rabon kayan abincin ciki har da hukumar HISBAH ta jiha da su maida hankali wajen aiwatar da aikin cikin gaskiya da rikon amana don cimma manufar shirin.

“Wannan shirin zai taimaka wajen rage saukaka rayuwa, a cewar Gwamnan Kano.

“Inda ya sake kara jinjina kaso mafi tsoka da jihar ta samu”.

Zouera Yousoufou dake zaman shugaban gidauniyyar ta Aliko Dangote tayi karin haske kan kokarin Alhaji Aliko Dangote wajen tallafawa al’umma, inda yace shakka babu gidauniyyar zata ci gaba da baiwa wannan bangaren muhimmanci.

“Mune a gidauniyyar Dangote muke ganin ya zama wajibi a sanar da al’umma irin kokarin da yake yi don sauran al’umma masu kudi su kwaikwayi halayensa na gari na tallafawa al’umma”, a cewar Yousoufou

Rabon tallafin kayan abincin da Alhaji Aliko Dangote ya jagoranta na shinkafa miliyan Daya dake dauke da kilo goma na nuni da kokarin shi wajen rage radadin rayuwa da marasa galihu ke fuskanta da kuma kara dankon zumunci a tsakanin al’umma.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai1 hour ago

Fasinjoji 85 Sun Tsallake Rijiya Da Baya A Wani Hatsarin Jirgin Sama A Senegal

Wani jirgin sama samfurin 737 dauke da mutane 85 ya tsallake rijiya da baya a filin jiragen sama na Dakar,...

Labarai1 hour ago

Za a Dauki Mataki Kan Masu Cin Zarafin Yan Aikin Gida

A wani mataki na kare hakkin ‘yan aikin gida da ma kare iyayen gidan da ake yi wa aikin daga...

Labarai2 hours ago

Majalisar Dattawan ta Amince da Hukuncin Kisa ga Masu Safarar Kwaya

Majalisar dattawan Najeriya ta amince da ƙudurin dokar hukuncin kisa ga masu safarar miyagun ƙwayoyi a faɗin ƙasar, bayan ƙudurin...

Labarai2 hours ago

Kotu ta Bayar da Belin Hadi Sirika kan Naira Miliyan 100

Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama na Nijeriya, Hadi Sirika ya musanta zargin aikata laifin almundahana da ya shafi kusan Naira...

Labarai1 day ago

Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila

Amurka ta sanar da batun dakatar da shirin ta na kai jirgi dauke da bamabamai zuwa Israila a cikin makon...

Labarai1 day ago

NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana

Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo ya karbi tawagar gani da ido...

Kasuwanci2 days ago

CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati

Babban Bankin Najeriya CBN ya bayar da wa’adin ranar 7 ga watan  Yulin 2024 ga masu POS su kammala rajista...

Fasaha2 days ago

Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno

  Gwamnatin jihar Borno ta fara aikin horas da malamai 1,949 a matakin farko da aka gano cewa suna iya...

Fasaha2 days ago

Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet

  Babban Bankin Najeriya (CBN) ya umurci bankunan kasar su fara cirar kaso 0.5 cikin 100 na duk kuɗin da...

Labarai2 days ago

An kashe Falasɗinawa 34,800 tun fara yaƙi – Ma’aikatar lafiyar Hamas

Ma’aikatar lafiya ta Hamas a Gaza ta ce an kashe Falasdinawa 34,789 a yankin tun ranar 7 ga watan Oktoba,...

Mafi Shahara