Connect with us

Labarai

Ma’aikatan Lafiya A Zamfara Sun Fara Yajin Aikin Gargadi Na Mako Guda

Published

on

Kungiyar Ma’aikatan Lafiya ta Najeriya (MHWUN), reshen Jihar Zamfara, ta ayyana yajin aikin gargadi na kwanaki bakwai bisa zargin wariya a aiwatar da tsarin albashi na musamman na ma’aikatan lafiya (CONMESS).

A wata sanarwa da mai magana da yawun kungiyar na jihar, Kwamared Shamsudeen Sadeeq ya sanya wa hannu, ma’aikatan sun zargi Kwamishinar Lafiya, Dr. Nafisa Mohammed Maradun, da aiwatar da tsarin CONMESS kashi 100 ga likitoci kawai, tare da watsar da sauran ma’aikatan lafiya.

Kungiyar ta ce ta gudanar da tarurruka da dama da jami’an gwamnati, ciki har da Kwamishinar Lafiyar, da Shugaban Ma’aikata na Jihar da Kwamishinan ’Yan Sanda, amma duk ba su haifar da Da mai ido ba.

Saboda haka kungiyar ta fara yajin aikin daga daren Laraba, 10 ga Satumba, zuwa 17 ga Satumba, 2025.

MHWUN ta umarci mambobinta a cibiyoyin lafiya na matakin farko, asibitocin gwamnati da na musamman su shiga  yajin aikin.

Ta kuma gargadi cewa, idan gwamnati ta kasa magance koke-koken su a wadannan kwanaki, za su shiga yajin aikin sai Baba-ta-gani.

A halin da ake ciki, gwamnatin jihar Zamfara ta roki kungiyar ta janye yajin aikin, tana mai bayyana shi a matsayin abin da bai dace da lokaci ba, musamman duba da annobar amai da gudawa da ke addabar al’umma.

A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na ma’aikatar lafiya, Suleiman Isah, ya fitar, Kwamishina Nafisa Maradun ta ce gwamnati ta sha alwashin inganta walwalar dukkan ma’aikatan lafiya.

Ta bayyana cewa gwamnatin Gwamna Dauda Lawal ta amince da karin albashi ga likitoci a matsayin wani bangare na shirin inganta walwalar ma’aikata.

Kwamishinar ta musanta zargin nuna son kai, tana mai cewa tattaunawa na gudana da masu ruwa da tsaki domin samar da ingantaccen tsari ga dukkan ma’aikatan lafiya.

Dr. Nafisa Maradun ta bayyana rashin jin dadinta kan matakin yajin aikin, tare da kira ga kungiyar ta koma kan teburin tattaunawa, inda ta tabbatar da cewa gwamnatin jihar a shirye take domin tattaunawa ta hanyar lumana don warware matsalolin da ke akwai.

 

Daga Aminu Dalhatu

Labarai

Labarai7 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara