Connect with us

Labarai

Karamar Hukumar Gwarzo Ta Raba Magunguna Da Kayan Aiki Ga Asibitoci

Published

on

A yunƙurinta na inganta harkar kiwon lafiya, Karamar Hukumar Gwarzo ta raba muhimman magunguna da kayan aikin  ga cibiyoyin kiwon lafiya a gundumomi 10.

An gudanar da bikin mika kayan a Cibiyar Musulunci ta Gwarzo, inda Shugaban Karamar Hukumar Dakta Mani Tsoho Abdullahi, wanda ya sami wakilcin mataimakinsa Alhaji Abdulmumin Garba Lakwaya, ya jagoranci taron.

Kayayyakin da aka raba sun haɗa da na’urar auna hawan jini, na gwajin siga, da wasu kayan aiki daban-daban da aka tanada domin ƙarfafa aikin cibiyoyin lafiya tare da faɗaɗa damar jama’a na samun ingantacciyar kulawa.

Yayin da yake jawabi, Lakwaya ya jaddada bukatar ma’aikata su jajirce wajen aiki da gaskiya da rikon amana. Ya tunatar da su cewa an samar da  kayayyakin ne domin amfanin marasa lafiya kai tsaye,  daidai da kudirin  karamar hukumar wajen samar da ingantaccien kiwon lafiya.

Mataimakin Shugaban ya kuma yaba wa Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, da kuma Dakta Gwarzo bisa ci gaba da ƙoƙarin inganta rayuwar jama’a.

Shi ma Kansilan Lafiya na Karamar Hukumar, Alhaji Nazifi Gambo Salihawa, ya jawo hankalin cibiyoyin lafiya kan bin ƙa’idojin rahoton lafiya na Najeriya, inda ya bukace su da su tabbatar da bin ka’ida wajen rubuta da kuma amfani da sabbin kayayyakin domin samun inganci, da kuma amincewar al’umma.

Wasu daga cikin shugabannin cibiyoyin da suka karɓi kayayyakin sun tabbatar da cewa za a raba magungunan bisa adalci tare da amfani da su yadda ya dace domin biyan bukatun lafiya na jama’a.

Taron ya samu halartar Kakakin Majalisar Karamar Hukumar, kansiloli, shugabannin cibiyoyin lafiya, da sauran masu ruwa da tsaki.

 

Daga Khadijah Aliyu

Labarai

Labarai15 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara