Labarai
Karamar Hukumar Gwarzo Ta Raba Magunguna Da Kayan Aiki Ga Asibitoci
A yunƙurinta na inganta harkar kiwon lafiya, Karamar Hukumar Gwarzo ta raba muhimman magunguna da kayan aikin ga cibiyoyin kiwon lafiya a gundumomi 10.
An gudanar da bikin mika kayan a Cibiyar Musulunci ta Gwarzo, inda Shugaban Karamar Hukumar Dakta Mani Tsoho Abdullahi, wanda ya sami wakilcin mataimakinsa Alhaji Abdulmumin Garba Lakwaya, ya jagoranci taron.
Kayayyakin da aka raba sun haɗa da na’urar auna hawan jini, na gwajin siga, da wasu kayan aiki daban-daban da aka tanada domin ƙarfafa aikin cibiyoyin lafiya tare da faɗaɗa damar jama’a na samun ingantacciyar kulawa.

Yayin da yake jawabi, Lakwaya ya jaddada bukatar ma’aikata su jajirce wajen aiki da gaskiya da rikon amana. Ya tunatar da su cewa an samar da kayayyakin ne domin amfanin marasa lafiya kai tsaye, daidai da kudirin karamar hukumar wajen samar da ingantaccien kiwon lafiya.
Mataimakin Shugaban ya kuma yaba wa Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, da kuma Dakta Gwarzo bisa ci gaba da ƙoƙarin inganta rayuwar jama’a.
Shi ma Kansilan Lafiya na Karamar Hukumar, Alhaji Nazifi Gambo Salihawa, ya jawo hankalin cibiyoyin lafiya kan bin ƙa’idojin rahoton lafiya na Najeriya, inda ya bukace su da su tabbatar da bin ka’ida wajen rubuta da kuma amfani da sabbin kayayyakin domin samun inganci, da kuma amincewar al’umma.

Wasu daga cikin shugabannin cibiyoyin da suka karɓi kayayyakin sun tabbatar da cewa za a raba magungunan bisa adalci tare da amfani da su yadda ya dace domin biyan bukatun lafiya na jama’a.
Taron ya samu halartar Kakakin Majalisar Karamar Hukumar, kansiloli, shugabannin cibiyoyin lafiya, da sauran masu ruwa da tsaki.
Daga Khadijah Aliyu
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai7 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai15 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
