Connect with us

Ilimi

UNICEF Ya Bukaci Jihar Kano Ta Bai Wa Yara Muhimmanci A Kasafin Kudi

Published

on

Asusun Kula da Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) ya nuna damuwa kan halin da yara ke ciki a jihar Kano, yana mai kira ga gwamnatin jihar da ta ƙara zuba jari a fannin lafiya, ilimi, da abinci mai gina jiki ta hanyar kasafin kuɗi da ya danganci makomar yara.

Shugaban ofishin UNICEF na Kano, Mista Rahma Rihood Muhammad Farah, ya bayyana hakan yayin wani taron tattaunawa da ‘yan jarida kan kasafin kuɗi mai la’akari da bukatun yara, inda ya gabatar da wasu alkalumma masu tayar da hankali dangane da rayuwar yara a jihar.

Farah ya ce jihar Kano na da yara fiye da miliyan 6 da rabi da ke ƙasa da shekaru 18, wadanda da dama daga cikinsu na fuskantar matsaloli masu tsanani kamar mace-macen yara, ƙarancin abinci mai gina jiki, da kuma rashin samun ingantaccen ilimi da kiwon lafiya.

Ya bayyana cewa, bisa ga rahoton MICS na 2021, yara 143,000 na mutuwa kafin su kai shekara biyar, yayin da kusan yara miliyan 2 da 900,000 ba su da cikakken rigakafi, sannan fiye da yara miliyan 4 na rayuwa cikin talauci.

Haka kuma, sama da yara miliyan 2 300,000 da suka kai shekarun makaranta suna zaune a gida ba tare da samun ilimi ba, wani hali da ya ce ya zama wajibi a sauya shi ta hanyar karfafa kasafin kuɗi na kula da yara.

Ya ce duk da wasu sauye-sauye da ake yi, fannin walwalar al’umma a Kano har yanzu na samun ƙarancin kudi, inda ya zargi sauyin kasafi da rashin daidaito a fannonin lafiya, ilimi da kare hakkin yara da janyo cikas ga cigaba.

Farah ya bayyana kasafin kuɗi mai kula da yara a matsayin wata dabara mai mahimmanci, fiye da ware kuɗi kawai ga makarantu da asibitoci.

A nasa jawabin, Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kano, Hon. Muhammad Bello Butu Butu, ya tabbatar da kudurin majalisar na tabbatar da cikakken aiwatar da kasafin kuɗi ga ma’aikatu da hukumomi.

Sai dai ya soki wasu shugabannin ma’aikatu da hukumomi da rashin kokarin karɓar kuɗaɗen da aka ware musu da kuma gazawar aiwatar da su, duk da kokarin bangaren zartarwa wajen sakin kudin. Ya bayyana cewa kimanin kashi 35% na kasafin kuɗin jihar na zuwa fannin lafiya ne da ilimi.

Masu ruwa da tsaki da suka halarci taron, ciki har da ‘yan jarida, kungiyoyin farar hula, da ma’aikatun gwamnati, sun yi kira ga gwamnatin Kano da ta tabbatar da kasafin kuɗi mai la’akari da yara, ta ƙara yawan kuɗaɗen da ake warewa shirye-shiryen kula da yara, tare da tabbatar da gaskiya da rikon amana a wajen aiwatar da kasafin.

 

Daga Khadijah Aliyu 

Labarai

Labarai12 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi12 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai13 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai15 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai1 day ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai2 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai3 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara