Labarai
An Kama Mutane 15 da ake Zargin Bature Tambaya Na Aiki Dasu Wajen Tada Zaune Tsaye A Kwara
Akalla mutane 15 da ake zargi da aikata laifuka ne aka kama bayan ci gaba da farmakin da ake kai wa wasu miyagu da ke da hannu wajen tabarbarewar tsaro a kananan hukumomin Edu da Patigi na jihar Kwara.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin, babban sakataren yada labarai na gwamna AbdulRazaq, Rafiu Ajakaye, ya ce wadanda ake zargin sun hada da wani bature mai suna Tambaya, a lokacin da aka shiga sabuwar tabarbarewar tsaro a yankin.
A cewarsa “Tambaya shi ne babban wanda ya kitsa harin da aka kai wa jami’an tsaro da ‘yan banga a Gada, Lafiagi.
Ya bayyana cewa an kama Tambaya da wasu mutane takwas a wata arangama da jami’an tsaro, yayin da aka kawar da wasu ‘yan kungiyarsa da dama.
Ajakaye ya kara da cewa “a yayin aikin, an kubutar da mutane biyu da aka kashe daga hannun wadanda ake zargin kuma an kwato N11m, wanda da alama kudaden ne na aikata laifuka.”
Ya ci gaba da cewa, matakin da gwamnatin jihar ta dauka kan masu aikata laifukan ya kasance a hannun gwamnatin jihar tare da hadin gwiwar ofishin mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, da kwamandojin tsaro na jiha, da kuma ‘yan banga.
ALI MUHAMMAD RABIU/ Kwara
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
