Labarai
An Yi Jana’izar Muhammadu Buhari A Gidansa Da Ke Daura
An bizne gawar tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, a gidansa da ke garin Daura.
Babban limamin Daura, Sheikh Hassan Yusuf ne ya jagoranci Sallar janazar a filin da ke kusa da gidan marigayin.
Bayan kammala sallar jana’izar, babban limamin Daura tare da Sarkin Daura, Alhaji Umar Faruk Umar, sun gabatar da addu’o’in neman rahama ga tsohon shugaban ƙasar.

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, da Firaministan Nijar Ali Lamine Zaine, da Shugaban Ƙasar Guinea-Bissau Umaru Sissoco, da tsohon Shugaban Ƙasar Nijar Muhammadou Issoufou, da Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Yemi Osinbajo sun halarci jana’izar.

Jakadu daga ƙasashe, sanatoci da ’yan majalisun jihohi da na tarayya, gwamnoni, ministoci, manyan ’yan kasuwa da shugabannin masana’antu daga sassa daban-daban na ƙasa sun halarci jana’izar domin girmama tsohon shugaban ƙasan.
Wakilanmu sun ruwaito cewa gagarumin cunkoson jama’a ya toshe dukkan hanyoyi masu shiga da fita daga Daura, musamman hanyar Mai’adua, inda gidan marigayin ya ke.

Tun da farko, Shugaba Tinubu tare da Shugaban Guinea Bissau da Firaministan Nijar sun karɓi gawar marigayi Muhammadu Buhari a filin jirgin sama na Umaru Musa Yaradua da ke Katsina, jim kaɗan bayan zuwanta daga Landan.
Shugaba Tinubu ya jagoranci faretin soja tare da hafsoshin soja na ƙasa, suka ɗauki gawar zuwa motar da aka tanadar don kai ta Daura. Sannan Shugaba Tinubu da baƙinsa suka raka gawar a cikin dogo jerin gwanon motoci.
Tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, wanda ya shugabanci Najeriya a matsayin soja da farar hula, ya rasu yana da shekaru tamanin da biyu (82) a duniya.
Daga Isma’il Adamu
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
