Connect with us

Ilimi

Dalibai Sama Da 200 Sun Sami Digiri Mai Daraja Ta Daya A FUD

Published

on

Jami’ar Tarayya ta Dutse (FUD) ta ce dalibai 209 za su karbi shaidar digiri mai daraja ta daya a taron yaye dalibai karo na 8 da na 9 da aka shirya gudanarwa a wannan wata.

Shugaban Jami’ar, Farfesa Abdulkarim Sabo Mohammed ne ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da ‘yan jarida kan shirye-shiryen da aka kammala domin taron yaye daliban a Dutse, Jihar Jigawa.

Ya ce, kididdigar yawan daliban da za a yaye ta nuna cewa, jimillar dalibai 1,271 sun samu digiri mai daraja ta biyu matakin farko(SecondClassUpper), yayin da dalibai 2,034 suka samu digiri mai daraja ta biyu,  mataki na biyu, kasa (Second Class Lower), sannan kusan dalibai 559 suka samu digiri mai daraja ta uku (Third Class).

Ya bayyana cewa, adadin jimillar daliban da za a yaye ya kai 4,277.

Farfesa Abdulkarim ya kara da cewa, adadin daliban da ke karatu a jami’ar ya karu daga 202 a shekarar 2011/2012 zuwa 18,000 a halin yanzu, tare da karuwar kwasa-kwasai daga guda 5 a 2011/2012 zuwa guda 45 a yau.

Shugaban Jami’ar ya bayyana cewa, za a gudanar da laccar taron yaye dalibai karo na 8 da 9, inda tsohon Shugaban Jami’ar na farko, Farfesa Jibrilla Dahiru Amin, zai gabatar da makala.

Ya ce taken laccar shi ne: “Amfani da Bincike da Kirkire-kirkire Domin Cimma Ci gaba mai Dorewa a Najeriya: Rawar da Manyan Makarantu Ke Takawa.”

Haka zalika, ya bayyana cewa, an kammala ginin sashen ilimin shari’a na jami’ar,  inda za a fara karbar dalibai a wannan sashe daga zangon karatu na gaba.

Ya ce, shirin kafa Sashen Kimiyyar Magunguna (Pharmaceutical Sciences) na daga cikin abubuwan da ake kan tsarawa a halin yanzu.

Farfesa Abdulkarim ya bayyana cewa, cikin shekaru hudu da suka gabata, jami’ar ta samu tallafin bincike fiye da Naira miliyan 800, ciki har da Naira miliyan 113 da kamfanin Google ya bayar domin kafa dakin binciken Artificial Intelligence(binciken kwakwaf ta yanar gizo), wanda shi ne na farko a cikin manyan makarantu a yankin Arewa maso Yamma.

Haka kuma, Farfesa Abdulkarim ya bayyana cewa, kwanan nan jami’ar  ta rattaba hannu kan yarjejeniya da Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya da Hukumar Samar da Wutar Lantarki ga Yankunan Karkara domin gina rukunin hasken rana na zamani mai karfin megawatt 1.6 wanda zai tabbatar da cewa harabar jami’ar za ta rika amfani da wutar lantarki ta hasken rana.

Ya kuma jaddada cewa daga cikin ayyukan da aka kammala a jami’ar akwai sabon ginin Majalisar makarantar(Senate Building), ginin sashen koyar da ilimin shari’a  (Faculty of Law), sabon dakin karatu(Library) , dakunan daukar darasi gudabiya masu cin daliba 250 kowannensu, da dakunan koyar da Kimiyya da Fasaha (STEM), da dakunan kwana guda biyu na mata da sauran su.

Farfesa Mohammed ya nuna godiyarsa ga ‘yan jarida a fadin jihar Jigawa da wajen jihar bisa hadin kai da goyon baya da suke baiwa jami’ar.

Daga karshe, ya yaba wa ma’aikatan jami’ar bisa hadin kai da jajircewarsu, yana mai cewa hakan ya taimaka wajen cimma nasarorin da Jami’ar ta samu.

Usman Muhammad Zaria

 

Labarai

Labarai18 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai2 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara