Connect with us

Labarai

Hajjin 2025: Sahun Farko Zai Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki 9 Ga Watan Mayu

Published

on

Sahun farko na Alhazan Najeriya zai tashi zuwa kasa mai tsarki a ranar 9 ga watan Mayun 2025.

Hakan na kunshe ne a cikin bayanin bayan taro da Hukumar Alhazai ta Kasa NAHCON, ta yi da Shugabannin Hukomomin Kula da Jin Daɗin Alhazai na Jihohi a  ranar 22 ga watan Afrilun 2025.

Manufar taron ita ce tantance matakin shirin da kowace Hukumar Alhazai ta Jiha ta kai.

Wata sanarwa da mataimakiyar daraktar watsa labarai ta hukumar NAHCON, Fatima Sanda Usara ta fitar, ta ce shugaban hukumar, Farfesa Abdullah Saleh Usman, ya tunatar da mahalarta taron cewa harkar Hajji na cikin matakin karshe na shirye-shirye kafin fara aikin Hajjin shekarar 2025.

Ya bukaci jihohi da su sanar da NAHCON matsayin da suka kai wajen samar da biza, rigakafi, sayen jakunkuna da sauran batutuwa  da suka jibancu aikin hajji.

A yayin taron, Kwamishinan Ayyuka na NAHCON, Prince Anofiu Elegushi, ya bayyana cewa kamfanin Air Peace  zai yi jigilar alhazai 5,128 daga jihohin Abia, Akwa Ibom, Anambra, Rundunar Sojoji, Bayelsa, Benue, Borno, Cross River, Delta, Ebonyi, Edo, Ekiti, Enugu, Imo, Kogi, Ondo, Rivers, da Taraba.

Yayin da kamfanin FlyNas zai dauki alhazai 12,506 daga Birnin Tarayya Abuja, Kebbi, Legas, Ogun, Osun, Sokoto da Zamfara. Kamfanin na FlyNas ya ware jirage tara domin gudanar da wannan aikin.

Sai kamfanin Max Air da zai dauki alhazai daga jihohin Bauchi, Gombe, Jigawa, Kano, Katsina, Kwara, Oyo da Filato.

Kamfanin na Max Air ya yi alkawarin kammala jigilar alhazai  15,203 zuwa ranar 24 ga Mayu, inda zai yi amfani da jirage biyu,  jirgin B747 mai daukar mutum 400, da wani mai daukar mutum 560.

Haka zalika, kamfanin Umza zai yi jigilar alhazai 10,163 daga jihohin Kaduna, Adamawa, Nasarawa, Neja da Yobe. Shi kuma zai yi amfani da jiragin B747 mai daukar mutum 477 da B777 mai daukar mutum 310.

Wadanda kamfanonin jiragen sama 4 za su yi jigilar alhazan Hajjin 2025 su 43,000.

Kwamishinan Tsare-tsare, Bincike, Kididdiga, Labarai da Ayyukan Laburare (PRSILS), Farfesa Abubakar Yagawal, ya bayyana wa mahalarta taron irin shirin da hukumar ta yi dangane da samar da asibitoci a Makka da Madina, rabon kati na Yellow Card ga jihohi, tare da tunatar da su da su guji yi wa mata masu ciki rijistar  aikin hajji.

Sanarwar ta kara da cewa yayin da aka cimma matsaya cewa ranar 9 ga Mayu za a fara tashi, ana kuma sa ran kammala jigilar a ranar 24 ga watan Mayu.

Har ila yau, sanarwar ta ce za a fara dawowa daga kasar mai tsarki a ranar 13 ga watan Yuni zuwa 2 ga watan Yuli, idan Allah ya yarda.

 

 

Safiyah Abdulkadir 

Labarai

Labarai11 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara