Kasuwanci
Zamu Tabbatar da Ingantuwar Depon Sojoji Na Zaria – Ministan Tsaro Badaru
Ministan Tsaro, Mohammed Badaru Abubakar ya yi alkawarin inganta sansanin horas da kuratan sojoji dake Zaria wato Depot domin baiwa hukumar Soji damar ci gaba da aikin horaswa a wajen.
Ministan ya yi wannan alkawarin ne a lokacin da ya kai ziyarar tantance sojojin Najeriya da ke Chindit Cantonment a Zariya.
Ministan ya kuma ce, ma’aikatar tsaro ba za ta bar wani abu ba, wajen tabbatar da cewa makarantar firamare ta Chindit ta samu ingantuwar kayan aiki don dacewa da tsarin zamani a matsayin hanyar kara kwarin gwiwa na hafsoshi da sojoji na Kantoment da ke amfana da wajen.
Ya kara da cewa ofishin sa zai hada kai da gwamnatin jihar Kaduna domin ganin an kammala makarantar sakandare ta Chindit.
Ministan ya kuma yi alkawarin taimakawa wajen hakar wasu rijiyoyin burtsatse masu amfani da hasken rana domin kara inganta rijiyoyin burtsatse da ke cikin Depot din domin rage kalubalen da ke tattare da samar da ruwan sha a yankin.
Da yake jawabi tun da farko, kwamandan, Depot, Manjo Janar Ahmed Mohammed ya gode wa ministan bisa wannan ziyara, sannan ya kuma sanar da shi yadda babban hafsan sojin kasa, Laftanar-Janar Olufemi Oluyede ya yi don magance kalubalen da ke fuskantar Depot din.
Ya kuma bayyana fatan cewa wannan hadin gwiwa zai sanya Depot a kan hanyar da ta dace don ganin ta cika aikinta na samarda sojojin Nijeriya.
Kwamandan ya bada tabbacin cewa za a kula da jin dadin ma’aikata da wadanda aka dauka yadda ya kamata domin tabbatar da cewa hukumar ta samu cikakkiyar damar cimma muradun Najeriya.
REL/HALIRU HAMZA
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
