Connect with us

Ilimi

Kwara Ta Gargadi Jama’a Akan Gine-Gine Akan Bututun Ruwa

Published

on

Gwamnatin jihar Kwara ta gargadi mazauna jihar kan yin gine-gine a kan bututun ruwa a fadin jihar.

 

Kwamishinan Albarkatun Ruwa na Jihar, Usman Yunusa Lade, ya yi wannan gargadin a lokacin da ya kai ziyarar duba aikin gyaran babban bututun ruwa dake Flower Garden, a Ilorin.

 

Kwamishinan, wanda ya samu wakilcin Sakatariyar Dindindin, Misis Christiana Asonibare, ta ce “kamar gine-gine, masallatai, coci-coci da shaguna a kan bututun ruwa da jama’a ke yi yana da illa ga samar da isasshen ruwa a fadin jihar.”

 

Yunusa -Lade ya yi kira ga daukacin mazauna yankin da su kara kaimi ga kokarin gwamnati ta hanyar yin la’akari da bututun ruwa kafin a gina wani gini domin kaucewa lalata bututun ruwa da hana ruwa gudu ga al’umma.

 

A nasa bangaren babban Injiniya mai kula da aikin gyaran bututun da aka gyara a lambun Flower, Bamidele Idowu, ya tabbatar da cewa an kammala gyaran kuma za a gudanar da gwajin domin tabbatar da cewa ba a samu matsala ba.

 

Idowu ya bada tabbacin cewa yankunan da suka hada da Flower Garden, Lajorin, Offa Road, Sabo-Oke, Amilengbe, Adualere, Isale-koko, Oja-Gboro, da Ipata da dai sauransu za su ci gajiyar kammala gyaran da zarar an fara aikin turo ruwa.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

Labarai

Labarai19 hours ago

Iran Da Amurka Za Su Ci Gaba Da Tattaunawa Kan Shirin Nukiliyar Tehran

Iran da Amurka za su shiga zagaye na biyu na tattauna batun taƙaita shirin nukiliyar Tehran a yau Asabar. Masu...

Labarai20 hours ago

Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Takurawa Mataimakin Shugaban Kasa Shettima

Fadar shugaban kasa ta musanta rahotannin da ke nuni da cewa an hana mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, GCON shiga...

Kasuwanci20 hours ago

‘Yan Sandan Sun Ceto Wasu Mutane Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta yi nasarar kubutar da wasu mutane shida da aka yi garkuwa da su, a...

Kasuwanci20 hours ago

Gwamna Abdulrazaq Ya Bukaci Kiristoci Da Su Tuna Da Darussan Lokacin Ista

Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bukaci Kiristoci da su yi tunani a kan darussa, muhimmaci, da kuma kyawawan dabi’u...

Kasuwanci20 hours ago

Shugaban Majalisar Neja Ya Mika Sakon Easter Ga Al’ummar Kirista.

Kakakin majalisar dokokin jihar Neja, Barr. Abdulmalik Sarkin-Daji, ya mika sakon taya murna ga al’ummar kiristoci a jihar da ma...

Kasuwanci20 hours ago

Rundunar ‘Yansan Nijeriya Za Ta Gudanar Atisaye Ga Jami’anta a Jigawa

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta sanar da cewa za ta gudanar da atisayen harbe-harbe ga sabbin ‘yan sanda a karamar...

Labarai20 hours ago

Sarakuna Suna Bada Gudunmuwa Wajen Samarda Lafiya Da Hadin Kan Kasa– Kungiyar Sarakunan Afirka

    Kungiyar Sarakunan Afirka ta jaddada muhimmancin gudunmuwar da Sarakuna ke badawa wajen tabbatar da hadin kai da zaman...

Labarai1 day ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ya Yi Bikin Easter Tare da Al’ummomin Kiristoci

  Makera, Jihar Kaduna – Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Rt. Hon. Yusuf Dahiru Liman, ya halarci bukukuwan Easter tare...

Fasaha2 days ago

Gwamnatin Trayya Zata Zamantar da Kayayyakin Watsa Labaran ta

Gwamnatin tarayya ta jaddada kudirinta na kawo sauyi da kuma zamanantar da kafafen yada labarai na Najeriya da watsa shirye-shirye...

Kasuwanci2 days ago

Hukumar NSCDC ta tura jami’an tsaro 415 domin aikin Easter a Zamfara.

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya (NSCDC) reshen jihar Zamfara, ta tura jami’ai 415 a fadin jihar domin tabbatar da...

Mafi Shahara