Connect with us

Kasuwanci

NLC a Zamfara sun Bada Wa’adin Kwanaki 14 a Aiwatar da Mafi Karancin Albashi

Published

on

Kungiyoyin kwadagon Najeriya NLC da TUC a jihar Zamfara sun bayar da wa’adin kwanaki 14 ga gwamnatin jihar, inda suka bukaci da a kawo karshen kura-kuran da aka samu wajen aiwatar da mafi karancin albashi na N70,000.

 

An sanar da wa’adin ne a wani taron manema labarai a Gusau bayan wani taron gaggawa da kungiyoyin kwadago suka yi.

 

Da yake jawabi a wajen taron, shugaban kungiyar NLC na jihar Zamfara, Malam Sani Halliru, ya bayyana rashin jituwar da ake samu wajen biyan albashin watan Maris a matsayin abin bakin ciki da damuwa ga ma’aikatan gwamnati.

 

“Ya zama dole mu kira wannan taron manema labarai saboda mun ji takaicin yadda gwamnatin jihar ke aiwatar da mafi karancin albashi,” in ji Halliru.

 

Ya kara da cewa tun da farko gwamnatin jihar ta kafa kwamitin da zai sa ido a kan yadda za a aiwatar da sabon albashin tare da tabbatar wa ma’aikata cewa za a fara aiki a watan Maris. Sai dai ya lura cewa albashin watan Maris da aka biya a baya-bayan nan ya gaza yadda ake tsammani.

 

“Wasu ma’aikata sun samu karin Naira 3,000 kacal, yayin da wasu suka samu N4,000, N5,000, ko kuma akalla Naira 7,000. Har ma fiye da haka, an cire wasu ma’aikatan ba bisa ka’ida ba daga cikin albashin ma’aikata.” Ya kara da cewa.

 

Malam Sani Haliru ya kuma bayyana lamarin a matsayin cin amana, ya kuma yi gargadin cewa, idan gwamnati ta gaza magance wadannan matsalolin nan da makonni biyu, kungiyoyin za su dauki mataki.

 

Shi ma da yake jawabi, Shugaban TUC, Sa’idu Mudi, ya koka kan yadda har yanzu Zamfara ce jiha daya tilo da ba ta fara aiwatar da mafi karancin albashi na N70,000.

 

“Dukkan shugabannin kwadago da ma’aikata a jihar sun ji takaicin gazawar gwamnati wajen cika alkawarin da ta dauka.

 

A cewar Mudi sun ji takaicin kwamitin da aka nada domin aiwatar da sabon albashin yaki yin aikin da ya dace.

 

Ya yi zargin cewa da gangan wasu mutane a cikin gwamnati ke yin zagon kasa wajen aiwatar da aikin tare da yin kira ga Gwamna Dauda Lawal da ya kaddamar da bincike kan lamarin tare da daukar matakin da ya dace.

COV/AMINU DALHATU

Labarai

Labarai19 hours ago

Iran Da Amurka Za Su Ci Gaba Da Tattaunawa Kan Shirin Nukiliyar Tehran

Iran da Amurka za su shiga zagaye na biyu na tattauna batun taƙaita shirin nukiliyar Tehran a yau Asabar. Masu...

Labarai20 hours ago

Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Takurawa Mataimakin Shugaban Kasa Shettima

Fadar shugaban kasa ta musanta rahotannin da ke nuni da cewa an hana mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, GCON shiga...

Kasuwanci20 hours ago

‘Yan Sandan Sun Ceto Wasu Mutane Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta yi nasarar kubutar da wasu mutane shida da aka yi garkuwa da su, a...

Kasuwanci20 hours ago

Gwamna Abdulrazaq Ya Bukaci Kiristoci Da Su Tuna Da Darussan Lokacin Ista

Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bukaci Kiristoci da su yi tunani a kan darussa, muhimmaci, da kuma kyawawan dabi’u...

Kasuwanci20 hours ago

Shugaban Majalisar Neja Ya Mika Sakon Easter Ga Al’ummar Kirista.

Kakakin majalisar dokokin jihar Neja, Barr. Abdulmalik Sarkin-Daji, ya mika sakon taya murna ga al’ummar kiristoci a jihar da ma...

Kasuwanci20 hours ago

Rundunar ‘Yansan Nijeriya Za Ta Gudanar Atisaye Ga Jami’anta a Jigawa

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta sanar da cewa za ta gudanar da atisayen harbe-harbe ga sabbin ‘yan sanda a karamar...

Labarai20 hours ago

Sarakuna Suna Bada Gudunmuwa Wajen Samarda Lafiya Da Hadin Kan Kasa– Kungiyar Sarakunan Afirka

    Kungiyar Sarakunan Afirka ta jaddada muhimmancin gudunmuwar da Sarakuna ke badawa wajen tabbatar da hadin kai da zaman...

Labarai1 day ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ya Yi Bikin Easter Tare da Al’ummomin Kiristoci

  Makera, Jihar Kaduna – Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Rt. Hon. Yusuf Dahiru Liman, ya halarci bukukuwan Easter tare...

Fasaha2 days ago

Gwamnatin Trayya Zata Zamantar da Kayayyakin Watsa Labaran ta

Gwamnatin tarayya ta jaddada kudirinta na kawo sauyi da kuma zamanantar da kafafen yada labarai na Najeriya da watsa shirye-shirye...

Kasuwanci2 days ago

Hukumar NSCDC ta tura jami’an tsaro 415 domin aikin Easter a Zamfara.

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya (NSCDC) reshen jihar Zamfara, ta tura jami’ai 415 a fadin jihar domin tabbatar da...

Mafi Shahara