Connect with us

Labarai

Gwamna Namadi Ya Kai Ziyarar Bazata Cibiyoyin Ciyar Da Abincin Azumi

Published

on

Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa ya kai ziyarar bazata ga wuraren bayar da abinci na Ramadan a babban birnin jihar domin duba yadda ake aiwatar da shirin ciyarwar.

Wakilinmu ya ruwaito cewa Gwamnan ya ziyarci cibiyoyi a Dundubus, da Karnaya, da Kaci da Limawa, dukkaninsu a kewayen birnin Dutse.

Yayin bincikensa, Malam Umar Namadi ya yaba wa wasu cibiyoyi bisa jajircewarsu da kishin tabbatar da cewa shirin ciyarwar Ramadan yana tafiya yadda ya kamata.

Sai dai kuma, ya nuna matukar rashin jin dadinsa bayan gano wasu matsaloli na rashin iya tafiyar da shirin a wasu wuraren bayar da abincin.

Gwamnan ya jaddada bukatar kiyaye gaskiya, da adalci da tsafta a yayin rarraba abincin, yana mai kira ga masu ruwa da tsaki da su gyara duk wasu kura-kurai nan take.

Namadi ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da kokarin tabbatar da cewa dukkan cibiyoyin ciyarwa na Ramadan suna aiki yadda ya dace, tare da girmama mutuncin al’umma.

Ya kuma tabbatar da cewa za a dauki matakan da suka dace domin inganta yadda ake gudanar da shirin da kuma magance duk wasu matsaloli da aka gano.

Gwamnan ya kuma bukaci hukumomin yankuna da shugabannin al’umma da su kara kaimi wajen sa ido domin tabbatar da aiwatar da shirin cikin tsari.

Ya jaddada cewa jin dadin al’umma na daga cikin manyan abubuwan da gwamnatinsa ke ba muhimmanci.

Usman Muhammad Zaria 

Labarai

Labarai18 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi18 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai19 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai20 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai2 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai3 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai3 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara