Labarai
Gwamna Namadi Ya Kai Ziyarar Bazata Cibiyoyin Ciyar Da Abincin Azumi
Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa ya kai ziyarar bazata ga wuraren bayar da abinci na Ramadan a babban birnin jihar domin duba yadda ake aiwatar da shirin ciyarwar.
Wakilinmu ya ruwaito cewa Gwamnan ya ziyarci cibiyoyi a Dundubus, da Karnaya, da Kaci da Limawa, dukkaninsu a kewayen birnin Dutse.

Yayin bincikensa, Malam Umar Namadi ya yaba wa wasu cibiyoyi bisa jajircewarsu da kishin tabbatar da cewa shirin ciyarwar Ramadan yana tafiya yadda ya kamata.
Sai dai kuma, ya nuna matukar rashin jin dadinsa bayan gano wasu matsaloli na rashin iya tafiyar da shirin a wasu wuraren bayar da abincin.
Gwamnan ya jaddada bukatar kiyaye gaskiya, da adalci da tsafta a yayin rarraba abincin, yana mai kira ga masu ruwa da tsaki da su gyara duk wasu kura-kurai nan take.

Namadi ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da kokarin tabbatar da cewa dukkan cibiyoyin ciyarwa na Ramadan suna aiki yadda ya dace, tare da girmama mutuncin al’umma.
Ya kuma tabbatar da cewa za a dauki matakan da suka dace domin inganta yadda ake gudanar da shirin da kuma magance duk wasu matsaloli da aka gano.
Gwamnan ya kuma bukaci hukumomin yankuna da shugabannin al’umma da su kara kaimi wajen sa ido domin tabbatar da aiwatar da shirin cikin tsari.
Ya jaddada cewa jin dadin al’umma na daga cikin manyan abubuwan da gwamnatinsa ke ba muhimmanci.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai4 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai2 days agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai6 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai5 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
