Connect with us

Fasaha

Cutuka Biyar Da Ake Ɗauka A Lokacin Zafi

Published

on

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗi a baya-bayan nan dangane da ƙaruwar yanayin zafi a sassan ƙasar, yayin da jihohi da dama suke fuskantar ƙarin matsanancin zafi.

Gargaɗin ya kuma nuna cewa, tsananin zafin da za a yi fama da shi cikin kwanaki uku ko huɗu masu zuwa wanda zai haddasa damuwar da yanayin na zafi kan haifar a jihohi goma sha tara na ƙasar daga yankin arewa ta tsakiya da yankin gabashin ƙasar.

Kan haka ne muka tuntuɓi likita domin ya yi mana ƙarin bayani game da cututtuka biyar da aka fi kamuwa da su a lokacin zafi da kuma hanyoyin kare kai.

Sanƙarau – Dakta Hassan Ibrahim, likita a asibitin Biba da ke jihar Kaduna ya ce cutar sanƙarau na faruwa ne galibi idan aka samu cunkoson jama’a a wuri ɗaya da ya haɗu da zafi.

A cewarsa, “ƙwayoyin cuta za su shiga jikin mutum sai su shafi ƙwaƙwalwa sai a samu irin wannan.”

Zazzaɓin cizon sauro – Likitan ya ce idan yanayin zafi ya zo, mutane suna yawan buɗe jikinsu domin su sha iska. Ya ce “mutane sun fi zama a waje lokacin faɗuwar rana, lokacin da sauro ke tasiri da tafiyar da maleriya.

Hakan yana yawan taso da cutar maleriya a jikin mutane, kamar yadda likitan ya faɗa.

Fesowar ƙuraje – A lokacin zafi ne ake yawan zufa lamarin da ke janyo fesowar ƙuraje a jikn mutane wanda a cewar Dakta Hassan, idan ba a kula da su ba, “aka yi irin wata sosawa, yana iya kawo ciwo da wata ƙwayar cuta za ta iya ratsawa.”

Amai da gudawa – Dakta Hassan ya ce a irin wannan lokaci na zafi ne aka fi samun ƙuda da ruɓewar abinci. Ya ce idan ba a kula da abincin da muke ci ba, aka bari ƙuda suka yi damalmala a kai, hakan zai iya kawo ciwo a ciki idan aka ci.

Ƙonewar ruwa a jiki – A irin wannan yanayin, jikin mutum na yawan bushewa musamman a tsakanin dattijai. A cewar likitan, abin da ke sa mutum ya ji ƙishirwa, idan mutum na da rauni, ba za su samu jikinsu ya ankarar da su cewa su sha ruwa ba, ana so a riƙa shan ruwa a kai a kai.

Hanyoyin kariya

Dakta Hassan Ibrahim ya ce muhimman matakan da ya kamata mutane su ɗauka wajen kare kansu daga kamuwa da cuta a lokacin zafi shi ne tabbatar da cewa ana samun yanayin “shiga da fita ta iska” ta hanyar buɗe taga a wuraren kwana da wuraren aiki da kuma rage cunkoson jama’a a wuri guda.

Ya kuma ce akwai buƙatar a riƙa amfani da gidan sauro idan za a kwanta domin kare kai daga kamuwa da cutar maleriya inda ya ce akwai buƙatar a taƙaita zama a waje da yamma.

A cewar likitan, babban matakin da ya kamata mutane su kiyaye shi ne na tabbatar da tsaftar abincin da za ake ci musamman ƴaƴan itatuwa da kuma tabbatar da tsaftar jiki.

Ƙarin wani matakin shi ne yawaita wanka a kai a kai domin rage yanayin zafi a jiki.

Sai kuma yawaita shan ruwa domin gujewa ƙonewar ruwa a jiki inda ya shawarci masu azumi da su yawaita shan ruwa da zarar sun yi buɗa baki.

Abin da ya sa aka fi kamuwa da cututtuka a yanayin zafi

Dakta Hassan Ibrahim ya bayyana cewa dalilin shi ne, galibin cututtuka sun fi haɓaka a lokacin zafi saboda yanayin tsaurin jiki da inda jiki ke tafiya.

“Jiki yana da yadda yake gyara kansa a duk yanayin da ya shiga, lokacin zafi yana zuwa masa da ƙarin matsi da yadda jikin zai fitar da zafi da inda zai riƙe daidai.” in ji likitan.

“A lokacin zafi, mun ƙara wa jikinmu aiki, saboda a ciki ɗumi gare shi kuma yana son ya riƙe ɗumi kuma a lokacin zafi, jikinmu yana ƙara aikin fitar da ɗumi waje yana kuma ƙoƙarin samun abin sanyi da zai iya daidaita yanayin da yake tafiyar da aikin.”

Likitan ya ce a irin wannan yanayi da jiki ke tsintar kansa a lokacin zafi, “akwai rauni da ke tasar da cutuka da za su yi tasiri.”

A cewar shi, kashi 90 na cututtuka a duniya yana da alaƙa da wani abu na sarari saboda akwai ƙwayoyin cuta da suka fi tasiri a yanayin zafi.

Labarai

Labarai24 hours ago

Tinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa

Daga Bello Wakili Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Lamido Abubakar Yuguda a matsayin Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa CBN,...

Labarai1 day ago

An Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau

Daga Aminu Dalhatu Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Kabir Yahaya Gusau a matsayin Darakta Janar na...

Labarai1 day ago

Kwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u  Hukumar Kwastam ta Kasa reshen Jihar Kwara ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta...

Labarai2 days ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai3 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi3 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai3 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai4 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai4 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai4 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Mafi Shahara