Connect with us

Ilimi

Tinubu Ya Umarci Dangote Da BUA Su Rage Farashin Siminti

Published

on

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya umarci kamfanin Dangote da BUA da su rage kudin farashin buhun siminti don samar wa al’umma sauki daga matsin rayuwa da ake fuskanta.

Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi ne, ya bayyana hakan ga manema labarai jim kadan bayan ziyara da ya kai masana’antar siminti ta BUA da ke Sakkwato a ranar Alhamis.

 

Babban Darakta a kamfanin BUA, Alhaji Kabiru, ya ce a halin yanzu suna sayar da buhun siminti kan kudi Naira 6000, don cika alkawarin da suka yi daukar wa shugaban kasa cewa ba za su sayar da buhun siminti sama da 7000 ba.

“Game da batun farashin siminti, zan iya cewa har yanzu suna yin abin da ya dace kamar yadda suka tattauna da shugaban kasa

“Shugaban kasa ya jaddada batun dawo da farashin baya domin saukaka wa talaka.

“Ina so na kara musu kwarin gwiwa don su bi umarnin shugaban kasa domin mu cimma shirin samar da gidaje da kuma sabbin hanyoyin gina rayuwa kamar yadda shugaban kasa ya bukata,” in ji shi.

A baya-bayan nan dai kayayyaki sun yi tashin gwauron zabi a Najeriya, lamarin da ya sanya talakawa kokawa.

Farashin kudin buhun siminti ya ninka kudinsa na baya, inda a wasu jihohi ake sayar da shi daga Naira 10,000 zuwa 15,000.

A gefe guda kuwa, kungiyoyin kwadago na NLC da TUC sun gudanar da zanga-zangar kwanaki biyu a ranar Talata da Laraba, don neman gwamnatin tarayya yi wani abu kan tsadar rayuwa a Najeriya.

Shugaba Tinubu dai ya roki ‘yan Najeriya da su kara hakuri kan yanayin da ake ciki, wanda a cewarsa yana aiki tukuru don samar wa da talaka sauki daga halin da ake ciki.

Labarai

Labarai11 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi11 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai12 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai13 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai1 day ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai2 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara