Labarai
Kotu Ta Bayar Da Umarnin Kamo Ado Gwanja
Wata Babbar Kotu a Jihar Kano, karkashin jagorancin Mai Sharia Aisha Mahmud, ta ba da umarnin kamo mawaki Ado Isa Gwanja.
Kotun ta kuma haramta wa mawakin yin waka har zuwa lokacin da ’yan sanda za su kammala bincike a kansa.
Wannan dai na zuwa ne bayan da Majalisar Malamai ta Jihar Kano, ta maka Ado Gwanja da wasu kara a kotu, kan amfani da kalaman da ba su dace ba a wakokinsu.
Aminiya ta tuntubi, shugaban Kungiyar Jarumai na Kannywood, Alhassan Kwalle, amma jarumin, ya ce ba shi da masaniya game da umarnin kotun na kamo Ado Gwanja.
Idan ba a manta ba a 2023, kotu ta gayyaci Ado Gwanja, Idirs mai wushirya, Murja Ibrahim Kunya, 442 da wasu bayan da wasu mazauna Kano suka maka su a kotu kan zargin bata tarbiyyar yara.
A baya-bayan nan, Hukumar Hisba ta jihar, ta kama tare da gurfanar da fitacciyar ’yar TikTok, Murja Ibrahim Kunya a kotun Musulunci da ke Unguwar PRP a jihar.
-
Labarai4 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai1 day agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai2 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai5 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
