Connect with us

Labarai

Rukunin Farko Na Alhazan Jihar Borno Ya Isa Madina

Published

on

Rukunin farko na maniyyata 383 daga jihar Borno ya isa garin kasa mai tsarki da safiyar yau Litinin tare da ragowar maniyyata 27 daga jihar Yobe.

Jihar Borno na da jimillar maniyyata 1,815 da ake sa ran za a yi jigilar su  zuwa aikin Hajjin bana.

Da yake jawabi ga rukunin na farko na maniyyatan a filin jiragin sama na Muhammadu Buhari da ke Maiduguri, mataimakin gwamnan jihar Borno, Alhaji Umar Kadafur ya bukace su da su bi dokokin kasar Saudiyya sau da kafa.

Ya kuma bukace su da su yi addu’ar samun dauwamamman zaman lafiya a jihar da kasa baki daya.

A wata hira da gidan rediyon Najeriya a Maiduguri, mukaddashin shugaban hukumar jin dadin alhazai ta jihar Borno, Alhaji Dawule Mainok ya ce rukunin na  farko ya kunshi maza 234 da mata 149.

Ya yi kira ga maniyyatan da su kasance jakadu nagari yayin da suke kasa mai tsarki.

Biyu daga cikin mahajjatan Aisha Ali daga Ngala da Idris Allamin daga karamar hukumar Konduga sun bayyana aikin tantancewar a matsayin maras cikas, sun yabawa hukumar alhazai ta kasa da hukumar alhazai ta jiha bisa jajircewa wajen ganin komi ya tafi yadda ake bukata.

Dauda Iliya

Labarai

Labarai12 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara