Connect with us

Labarai

Mutane Sama Da 100 Sun Mutu A Fadan Da Ya Barke A Sudan

Published

on

An kwashe sama da makwanni biyu ana gwabza fada tsakanin sojojin Sudan da wata fitacciyar kungiyar sa-kai kan wani babban birnin da ke yammacin yankin Darfur inda aka kashe akalla mutum 123, in ji wata kungiyar agaji ta kasa da kasa a ranar Lahadi.

Yakin da aka yi a el-Fasher, babban birnin lardin Darfur ta Arewa, ya kuma raunata fiye da mutum 930 a lokaci guda, in ji kungiyar likitocin kasa da kasa ta Doctor’s Without Borders.

Wannan alama ce ta tsananin tashin hankali,” in ji kungiyar. “Muna kira ga bangarorin da ke fada da juna da su kara kaimi wajen kare fararen hula“.

Sabon rikici tsakanin sojoji da dakarun sa-kai ya barke ne a farkon watan nan a birnin, wanda ya tilastawa dubban mutane barin gidajensu, a cewar Majalisar Dinkin Duniya.

El-Fasher ya zama cibiyar rikici tsakanin sojoji da RSF, wanda ke samun taimakon mayakan Larabawa da aka fi sani da Janjaweed.

Birnin dai shi ne tunga ta karshe da har yanzu sojoji ke rike da shi a yankin na Darfur.

Rikicin Sudan dai ya faro ne a watan Afrilun bara lokacin da rikici ya barke tsakanin shugabannin sojoji da na RSF a babban birnin kasar, Khartoum, da sauran wurare a kasar.

Labarai

Labarai12 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara