Labarai
Mutane Sama Da 100 Sun Mutu A Fadan Da Ya Barke A Sudan
An kwashe sama da makwanni biyu ana gwabza fada tsakanin sojojin Sudan da wata fitacciyar kungiyar sa-kai kan wani babban birnin da ke yammacin yankin Darfur inda aka kashe akalla mutum 123, in ji wata kungiyar agaji ta kasa da kasa a ranar Lahadi.
Yakin da aka yi a el-Fasher, babban birnin lardin Darfur ta Arewa, ya kuma raunata fiye da mutum 930 a lokaci guda, in ji kungiyar likitocin kasa da kasa ta Doctor’s Without Borders.
“Wannan alama ce ta tsananin tashin hankali,” in ji kungiyar. “Muna kira ga bangarorin da ke fada da juna da su kara kaimi wajen kare fararen hula“.
Sabon rikici tsakanin sojoji da dakarun sa-kai ya barke ne a farkon watan nan a birnin, wanda ya tilastawa dubban mutane barin gidajensu, a cewar Majalisar Dinkin Duniya.
El-Fasher ya zama cibiyar rikici tsakanin sojoji da RSF, wanda ke samun taimakon mayakan Larabawa da aka fi sani da Janjaweed.
Birnin dai shi ne tunga ta karshe da har yanzu sojoji ke rike da shi a yankin na Darfur.
Rikicin Sudan dai ya faro ne a watan Afrilun bara lokacin da rikici ya barke tsakanin shugabannin sojoji da na RSF a babban birnin kasar, Khartoum, da sauran wurare a kasar.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
