Connect with us

Ilimi

Talatar Nan Jirgin farko na Maniyatan jihar Kwara Zai Tashi

Published

on

An dage tashin jirgin farko daga filin jirgin sama na Janar Tunde Idiagbon na kasa da kasa na Ilorin don gudanar da aikin hajjin bana na 2024 zuwa Saudiyya a ranar Talata 21 ga watan Mayu.

 

Sanarwar da Babban Sakataren Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kwara, Alhaji Abdulkadir Abdulsalam ya fitar, ta ce an samu canjin ranar ne sakamakon tsaikon da aka samu daga bangaren NAHCON da kamfanonin jiragen sama.

 

A cewar sanarwar Alhazan jihar Kwara da farko an shirya yin jigilarsu na farko a ranar Litinin 20 ga Mayu, 2024.

 

Sanarwar ta shawarci maniyyatan su zo sansanin alhazai litinin din kafin fara jigilar su a ranar Talata da karfe 10:20 na safe.

 

A halin da ake ciki Mai Martaba Sarkin Ilorin Alhaji Ibrahim Sulu-Gambari ya bukaci maniyyatan da su yi amfani da lokacin gudanar da aikin Hajjin bana wajen gudanar da addu’o’i na musamman domin samun zaman lafiya, hadin kai da ci gaban tattalin arzikin kasa.

 

Alhaji Sulu-Gambari ya bayyana haka ne a sakon sa na fatan alheri ta hannun mai magana da yawunsa, Mallam Abdulazeez Arowona.

 

Ya kuma umarce su da su yi amfani da damar ziyarar da zasu kai garuruwan Madina da Makkah na kasar Saudiyya a wannan lokaci mai albarka a matsayin babban abin alfahari na neman kusanci ga Allah Madaukakin Sarki.

 

Mai martaba Sarkin ya roki Allah Madaukakin Sarki da Ya ba dukkan alhazai lafiya da basira domin gudanar da ayyukan Hajji cikin nasara.

 

REL/ALI MUHAMMAD RABIU/Wababe

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara