Labarai
Shugaba Tinubu Ya Taya Mahamat Déby murnar lashe zaɓen Chadi
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya taya zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Chadi, Mahamat Déby murnar nasarar lashe zaɓen shugaban ƙasar da aka gudanar a makon da ya gabata.
Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar, Ajuri Ngelale ya fitar, shugaba Tinubu ya ce nasarar gudanar da zaɓen da aka yi a ƙasar ya nuna irin kishin da al’umma da gwamnatin Chadi ke da shi wajen mayar da ƙasar kan tsarin mulkin dimokraɗiyya.
Shugaban na Najeriya ya kuma tabbatar wa da zaɓaɓɓen shugaban Chadin cewa Najeriya za ta ci gaba da aiki kafaɗa da kafaɗa da ƙasar, a yayin da ya ce duka ƙasashen biyu ke naman bunƙasa zaman lafiya da tsaro da ci gaba al’umomin ƙasashen.
Sanarwar ta kuma ce shugaba Tinubu ya yi kiran ci gaba da aiki tare da haɗin kai tsakanin ƙasashen biyu.
Shugaba Tinubu ya kuma yi fatan alƙairi ga Mahamat Déby a tsawon wa’adin mulkinsa.
Bello Wakili/Wababe
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
