Connect with us

Labarai

Milk Value Chain Foundation Da CORET Sun Horasda Mata Harkar Kiwo Da Sarrafa Madara A Kaduna

Published

on

Gidauniyar Inganta Madara (Milk Value Chain Foundation) tare da haɗin gwiwar Kungiyar Hadin Kan Masu Kiwon Gargajiya ta Africa, wato CORET, sun shirya taron karawa juna sani domin inganta harkar kiwo da samar da isasshen madara a Najeriya, tare da bai wa matasa da mata damar dogaro da kai.

Taron wanda ya gudana a garin Kaduna, ya mayar da hankali kan horar da mahalarta kan sabbin hanyoyin kiwon dabbobi, dabarun samar da ciyarwa, da kuma yadda za su inganta sarrafa madara domin samun ci gaba mai ɗorewa.

Shirin ya samu goyon bayan ƙungiyar tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka, ECOWAS, da kuma tallafin kuɗi daga gwamnatin Swiss Cooperation.

Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban Gudanarwan CORET, Dr. Abdu Umar Hardo, ya bayyana cewa wannan shiri yana da nufin sauya tsarin kiwon gargajiya zuwa na zamani, tare da samar da damammakin tattalin arziki ga matasa da mata musamman a cikin al’ummomin makiyaya.

Dr. Ardo ya ce aiwatar da wannan shiri da gaske zai taimaka wajen rage zaman kashe wando da matsalar rashin aikin yi, ba kawai a Jihar Kaduna ba har ma da Najeriya baki ɗaya.

Haka zalika, wakilar gidauniyar Milk Value Chain Foundation, Dr. Bilkisu Yusuf, ta yaba da hadin gwiwar, tare da jaddada muhimmancin amfani da ilimin da mahalarta suka samu domin amfanar al’ummarsu.

A kasidarsa mai taken “Inganta Halittar Dabbobi Don Kara Yawan Madara a Najeriya”, Dr. Sabo Mohammed Abubakar ya bukaci gwamnati a matakai daban-daban da ta zuba jari a fannin kiwo da samar da ciyawa mai inganci domin bunkasa tattalin arzikin kasa.

Wani jami’i daga Hukumar Bada Ilimin Makiyaya ta Kasa, Alhaji Abubakar Lawal Boro, ya bayyana taron a matsayin muhimmin ci gaba wanda zai zama madogara ga makiyaya, tare da fatan shirin zai ci gaba da gudana don tallafa musu da kuma ƙarfafa tattalin arzikin ƙasa.

Shugaban al’umma na Ladugga, Madakin Ladugga, Alhaji Salihu Yunusa, ya bayyana jin daɗinsa da yadda mambobinsa suka amfana da horon, musamman wajen fahimtar yadda za su inganta hanyoyin tara da sayar da madara.

Daga cikin masu gabatar da kasidu akwai Malam Attahiru Alhassan Jaoji daga Jami’ar Ahmadu Bello Zaria, wanda ya gabatar da makala kan “Manufofi da Tsokaci Kan Shirin Sarrafa Madara a Yammacin Afirka,” da kuma Jonathan Jatau wanda ya yi bayani kan dabarun bunkasa yawan madara ta hanyar inganta halittar dabbobi.

Mahalarta taron sun fito ne daga yankunan Damau, Ladugga da Luma Kwasam, dukkansu daga cikin Jihar Kaduna.

Cov: Adamu Yusuf

Labarai

Labarai3 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi3 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai3 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai5 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai1 day ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai2 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara