Labarai
Ƙungiyar NUJ–FRCN Kaduna Ta Kaddamar da Tallafin Ramadan ga Mambobinta
Kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya reshen gidan rediyon tarayyar Kaduna, ta raba buhunan shinkafa da sukari ga mambobinta a matsayin tallafin domin saukaka musu a lokacin azumin Ramadan.
Shugaban kungiyar Umar Adamu Sarkinfada ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a harabar gidan Rediyon Najeriya Kaduna da ke Kaduna.
Ya ce an dauki matakin ne domin rage wahalhalun da tsadar kayan abinci ke haifarwa, musamman a lokacin watan Ramadan da kudaden kayayyakin masarufi ke karuwa.
A cewarsa, duk da cewa kayayyakin ba za su cika bukatun membobin ba, an yi su ne don samar da dan agaji da kuma zama wata alama ta nuna godiya ga goyon baya da hadin kai da shugabancin ya samu.

Shugaban ya kuma yi bukaci mambobin kungiyar da su ci gaba da ba su goyon, ya kuma yi kira ga Musulmi da Kirista da su yi amfani da lokutan Ramadan da na Azumi wajen yi wa kasa addu’ar zaman lafiya, hadin kai, da wadata.
Wasu da suka ci gajiyar shirin sun yabawa kwamitin zartarwar kungiyar bisa wannan shiri tare da karfafa gwiwar shugabanni da su ci gaba da gudanar da ayyukansu na walwala tare da inganta hadin kai a tsakanin mambobin kungiyar.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
