Connect with us

Ilimi

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Published

on

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark, AP Moller-Maersk, domin fadada ayyukan tashar jiragen ruwa da ake da su da karin ayyukan jigilar kaya a tashoshin jiragen ruwa na Najeriya.

 

Shugaban Kamfanin A.P Moller-Maersk, Mista Robert Maersk Uggla ne ya bayyana hakan a yayin ganawarsa da Shugaba Tinubu a gefen taron tattalin arzikin duniya na musamman kan hadin gwiwa, ci gaba da makamashi a birnin Riyadh na kasar Saudiyya.

 

Shugaba Tinubu ya bayyana cewa zuba jarin zai taimaka wajen sake gina tashoshin jiragen ruwa a sassan gabashi da yammacin Najeriya.

 

Shugaban ya ce, hakan zai kara tallafawa kokarin sabunta tashoshin jiragen ruwa na kasar nan, da nufin inganta harkokin kasuwanci, da saukaka shigo da kayayyaki, da rage cin hanci da rashawa a tashoshin jiragen ruwa, tare da inganta harkokin kasuwanci.

 

 

Shugaban ya tabbatar wa Maersk kudirin gwamnatinsa na hada kai da samar da yanayin da zai sa ‘yan kasuwa su bunkasa a kasar.

 

Ya ba da misali da hadin gwiwar da Maersk ta yi a baya wajen bunkasa tashar ajiye sundukai ko kwantainoni a Jihar Ogun a matsayin wata shaida ta hadin gwiwa mai inganci tare da kamfanin hada-hadar kayayyaki.

 

Da yake karin haske game da dadewar da kamfanin Maersk ke yi a Najeriya da kuma yadda ya yi imani da makomarsa, Shugaban Kamfanin A.P Moller-Maersk, Mista Robert Maersk Uggla ya ce kamfaninsa ya zuba jarin sama da dala miliyan dubu 2 a tashoshin jiragen ruwa na Najeriya da sauran ayyuka.

 

Ya kuma jaddada yiwuwar tashoshin jiragen ruwa na Najeriya za su iya daukar manyan manyan jiragen ruwa, sannan ya jaddada bukatar fadada ayyukan tashar jiragen ruwa domin biyan bukata, tare da rage tsadar kayayyaki.

 

“Mun yi imani da Najeriya, kuma za mu zuba jarin dala miliyan 600 a kayayyakin nan da kuma sanya tashoshin jiragen ruwa su zama masu daukar manyan jiragen ruwa.

Bello Wakili/Wababe

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara