Ilimi
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark, AP Moller-Maersk, domin fadada ayyukan tashar jiragen ruwa da ake da su da karin ayyukan jigilar kaya a tashoshin jiragen ruwa na Najeriya.
Shugaban Kamfanin A.P Moller-Maersk, Mista Robert Maersk Uggla ne ya bayyana hakan a yayin ganawarsa da Shugaba Tinubu a gefen taron tattalin arzikin duniya na musamman kan hadin gwiwa, ci gaba da makamashi a birnin Riyadh na kasar Saudiyya.
Shugaba Tinubu ya bayyana cewa zuba jarin zai taimaka wajen sake gina tashoshin jiragen ruwa a sassan gabashi da yammacin Najeriya.
Shugaban ya ce, hakan zai kara tallafawa kokarin sabunta tashoshin jiragen ruwa na kasar nan, da nufin inganta harkokin kasuwanci, da saukaka shigo da kayayyaki, da rage cin hanci da rashawa a tashoshin jiragen ruwa, tare da inganta harkokin kasuwanci.
Shugaban ya tabbatar wa Maersk kudirin gwamnatinsa na hada kai da samar da yanayin da zai sa ‘yan kasuwa su bunkasa a kasar.
Ya ba da misali da hadin gwiwar da Maersk ta yi a baya wajen bunkasa tashar ajiye sundukai ko kwantainoni a Jihar Ogun a matsayin wata shaida ta hadin gwiwa mai inganci tare da kamfanin hada-hadar kayayyaki.
Da yake karin haske game da dadewar da kamfanin Maersk ke yi a Najeriya da kuma yadda ya yi imani da makomarsa, Shugaban Kamfanin A.P Moller-Maersk, Mista Robert Maersk Uggla ya ce kamfaninsa ya zuba jarin sama da dala miliyan dubu 2 a tashoshin jiragen ruwa na Najeriya da sauran ayyuka.
Ya kuma jaddada yiwuwar tashoshin jiragen ruwa na Najeriya za su iya daukar manyan manyan jiragen ruwa, sannan ya jaddada bukatar fadada ayyukan tashar jiragen ruwa domin biyan bukata, tare da rage tsadar kayayyaki.
“Mun yi imani da Najeriya, kuma za mu zuba jarin dala miliyan 600 a kayayyakin nan da kuma sanya tashoshin jiragen ruwa su zama masu daukar manyan jiragen ruwa.
Bello Wakili/Wababe
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
