Connect with us

Labarai

Zabe Babu Hamayya: Isma’il Dutse Ya Karbi Ragamar NUJ Jigawa

Published

on

An zabi Comrade Isma’il Ibrahim Dutse na ma’aikatar yada labarai a matsayin sabon shugaban kungiyar ‘yan jaridu NUJ ta kasa reshen jihar Jigawa ba tare da hamayya ba.

A lokacin da yake sanar da sakamakon zaben, mataimakin shugaban kungiyar na kasa mai kula da shiyya ta daya wato Zone A, Comrade Tukur Umar Muhammad ya ce an kuma zabi Nura Sani Bello da Najib Umar da Aminu Umar Shuwajo ba tare da hamayya ba.

Tukur ya ce Aisha Abba Ahmed ta kamfanin dillancin labarai na kasa NAN dake Dutse ta samu nasara da yawan kuri’u 46, shi kuma Abdullahi Mukhtar ya sami kuri’u 34, yayin da Larai Musa na NTA ta sami kuri’u 14.

Tukur Umar, ya bayyana Aisha Abba Ahmed a matsayin wacce ta sami nasara a zaben da ta zamo sakatariyar kungiyar NUJ a jihar Jigawa.

Kazalika, Auwal Muhammad Kazaure ya samu nasara da kuri’u 69 akan Habibu Yusuf Adamu Babura wadda ya sami kuri’u 27.

A don haka, Mataimakin Shugaban na NUJ ya bayyana Auwal Muhammad Kazaure a matsayin ma’ajin kungiyar.

Sakataren kungiyar na shiyyar Zone A, Comrade Abdulrazak Bello Kaura ne ya rantsar da sabbin shugabannin nan take.

A jawabinsa, sabon shugaban kungiyar NUJ reshen jihar Jigawa, Isma’il Ibrahim Dutse ya bayyana zaben sa ba tare da hamayya ba a matsayin wani babban karimci da aka nuna masa.

Ya kuma yabawa masu ruwa da tsaki ciki har da Gwamna Umar Namadi bisa gudummawar da su ka bayar wajen samun nasarar zaben da aka gudanar cikin kwanciyar hankali da lumana.

Wakilinmu ya aiko mana da rahoton cewar, wadanda su ka halarci taron, sun hada da kwamishinan yada labarai, al’adu da matasa, Alhaji Sagir Musa Ahmed, da tsoffin shugabannin kungiyar, Alhaji Sabo Abdullahi Guri da Alhaji Mati Ali da wakilan sakataren Gwamnati da na shugaban ma’aikata da kuma Shugaban gidan Radiyon Tarayya Horizon FM, Dr Musa Idris Barnawa.

Kungiyar dai ta gudanar da taro karo na 8 wanda ya wakana a sakatariyar kungiyar da ke Dutse, babban birnin jihar.

Bayan kammala zaben, Shugabannin Kungiyar ta kasa, sun kai ziyarar ban girma gidan gwamnatin jihar domin gabatar da sabbin shugabannin kungiyar na jihar ga babban jami’in yada labarai na Gwamnan Jihar, Hamisu Mohammed Gumel.

 

Usman Mohammed Zaria

Labarai

Labarai6 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara