Connect with us

Labarai

‘Yan Kwana-Kwana A Kano Sun Ceto Rayukan Mutane 8 A Watan Mayu

Published

on

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta ce mutane 8 ne suka rasa rayukansu a sanadiyyar bala’o’i daban-daban a cikin watan Mayun 2024.

 

Jami’in hulda da jama’a na hukumar Saminu Yusif Abdullahi ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Kano.

 

A cewarsa, hukumar kashe gobara ta jiha karkashin jagorancin Alhaji Hassan Muhammad ta ceci rayuka 10 da dukiyoyi na sama da naira miliyan 8.

 

Jami’in hulda da jama’a ya bayyana cewa kiyasin kadarorin da aka yi asarar sun kai nai 31,650, 700 a cikin watan da ake magana.

 

Saminu ya yi nuni da cewa, hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta samu kiraye-kirayen kashe gobara guda 51, kirar ceto 13 da kuma kararrawar karya 6 a dukkan gidajen kashe gobara 29 da ke jihar.

 

Ya ce an samu raguwar yawan tashin gobara yayin da jihar ta samu rahoton afkuwar gobara guda 222 a sassan jihar tsakanin watan Janairu zuwa Maris 2024.

 

Jami’in hulda da jama’a ya lura cewa al’amuran da aka nada sun shafi gidajen zama, shaguna da gidajen mai.

 

Ya bukaci jama’a da su kiyaye tsaro a kowane lokaci tare da kai rahoton duk wani bala’i ga ofishin hukumar kashe gobara mafi kusa ko ta layukan wayar sa hukumar.

 

“Zan yi amfani da wannan damar wajen jawo hankalin jama’a da su kula da gobarar a hankali don gujewa afkuwar gobara.”

 

“Duk mai ababen hawa su rika tuki cikin kulawa tare da bin dokar hanya domin gujewa hadurran mota”.

 

KHADIJAH ALIYU/Wababe

Labarai

Labarai14 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara