Labarai
‘Yan Kwana-Kwana A Kano Sun Ceto Rayukan Mutane 8 A Watan Mayu
Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta ce mutane 8 ne suka rasa rayukansu a sanadiyyar bala’o’i daban-daban a cikin watan Mayun 2024.
Jami’in hulda da jama’a na hukumar Saminu Yusif Abdullahi ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Kano.
A cewarsa, hukumar kashe gobara ta jiha karkashin jagorancin Alhaji Hassan Muhammad ta ceci rayuka 10 da dukiyoyi na sama da naira miliyan 8.
Jami’in hulda da jama’a ya bayyana cewa kiyasin kadarorin da aka yi asarar sun kai nai 31,650, 700 a cikin watan da ake magana.
Saminu ya yi nuni da cewa, hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta samu kiraye-kirayen kashe gobara guda 51, kirar ceto 13 da kuma kararrawar karya 6 a dukkan gidajen kashe gobara 29 da ke jihar.
Ya ce an samu raguwar yawan tashin gobara yayin da jihar ta samu rahoton afkuwar gobara guda 222 a sassan jihar tsakanin watan Janairu zuwa Maris 2024.
Jami’in hulda da jama’a ya lura cewa al’amuran da aka nada sun shafi gidajen zama, shaguna da gidajen mai.
Ya bukaci jama’a da su kiyaye tsaro a kowane lokaci tare da kai rahoton duk wani bala’i ga ofishin hukumar kashe gobara mafi kusa ko ta layukan wayar sa hukumar.
“Zan yi amfani da wannan damar wajen jawo hankalin jama’a da su kula da gobarar a hankali don gujewa afkuwar gobara.”
“Duk mai ababen hawa su rika tuki cikin kulawa tare da bin dokar hanya domin gujewa hadurran mota”.
KHADIJAH ALIYU/Wababe
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai14 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
