Connect with us

Labarai

Yadda azumin bana ya riski al’ummar musulmi a sassan duniya

Published

on

Muslims wait to have their Iftar meal during the month of Ramadan at Al-Rajhi mosque in Riyadh June 21, 2015. REUTERS/Faisal Al Nasser

Ba kamar yadda aka saba  a baya ba, a bana an ga watan na Ramadan akan lokaci a kusan dukannin kasashen duniya, lamarin da ke tabbatar da yau Litinin matsayin daya ga watan na Ramadan.

Azumin na bana ya riski al’ummar musulmi kusan biliyan 2 a fadin duniya a yanayi daban-daban da ya shafi matsin tattalin arziki, tsadar rayuwa da kuma yake-yake.

Yadda Azumin ya riski ‘yan Africa

A kasashe irin su Najeriya, Nijar, Kamaru da Chadi da ke yammacin Africa jama’a sun fara azumin cikin karuwar rashin tsaro, matsanancin talauci, sauyin yanayi da kuma tsadar rayuwa da ke walagigi da mutanen su.

Kasashen da ke cikin na kan gaba masu yawan al’ummar musulmi a nahiyar Africa na fatan gwamnatoci zasu yi ruwa da tsaki wajen kawo karshen wadannan matsaloli.

A yankin gabashin Africa ma kusan haka abin yake, inda azumin ya riski kasashe irin su Kenya, Uganda da Rwanda cikin mastin tattalin arziki da tsadar rayuwa, su kuwa al’ummar jamhuriyar dimokradiyyar Congo sun marabci azumin cikin fargabar yaki da tashin hankali da kuma hare-haren M23 da sauran kungiyoyin masu rike da makamai.

Duk da kiraye-kirayen kasashen duniya, amma har yanzu babu wata tartibiyar yarjejeniyar tsagaita wuta a tsakanin bangarorin da ke rikici a Sudan mai yawan al’ummar musulmi, lamari da ba shakka zai kara tsananta azumin ga jama’ar su.

Masar, Habasha da Somalia suma dai duk babu wani sauyi game da rikive-rikice tsakanin ‘yan tawaye da dakarun gwamnati da kuma tsananin talauci da ke addabar ‘yan kasar.

Yadda Azumin ya riski gabas ta tsakiya

Duk da yadda wannan yanki na duniya yayi kaurin suna wajen rashin zaman lafiya, amma jama’a sun jima basu fara azumi ciki fargaba da rashin tabbas irin na bana ba, wannan kuwa ya faru ne saboda ruwan wutar da Isra’ila da shafe wattani biyar tana yi a Gaza, da kuma martani ta hanyar kai hari da mayakan Houthi na Lebanon ke kaiwa jiragen ruwan kasashe da ke yunkurin shigar da kaya Isra’ila ta kan tekun Maliya, yayin da wannan yaki ke barzanar fantsama zuwa sauran kasashe makwafta.

Ko a tattaunawar da aka zauna juma’ar da ta gabata tsakanin Hamas da Isra’ila an tashi ne baram-baram ba tare da cimma wata yarjejeniyar tsagaita wuta saboda  Ramadan din ba.

Isra’ila ta sha alwashin ci gaba da barín wuta, ba tare da la’akari da masu azumin ba, har sai Hamas ta bi dukannin ka’idojin da ta gidaya mata, dokokin da Hamas ta yi fatali da su.

Kasashe a wannan yanki na ci gaba da zaman doya da manja, ganin yadda aka ki fitowa kiri-kiri a nuna goyon baya ko akasin haka ko kuma kira ga Isra’ila da tsagaita wuta.

Yaya aka fara azumi a Turai

Turawan yammacin duniya ma ba’a bar su a baya ba wajen fara azumin na bana ba duk kuwa da fargabar rashin ingantaccen tsaro a kasashe irin su Faransa da Amurka, yayin da ake fama da matsin tattalin arziki a Burtaniya da makwaftanta sai kuma tsadar rayuwa da Belgium da Jamus da sauran su.

Azumin bana a yankin Asia

Yankin Asia da ya kunshi kasashe irin su China, Japan, Koriya da sauran su a iya cewa azumin na bana ya riski jama’a da sauki-saukin rayuwa, idan an kwatanta da sauran sassan duniya, duk da rikicin kan iyaka da ke tashi lokaci-lokaci tsakanin China da Taiwan, sai kuma gwaje-gwajen muggan makamai da Koriya ta arewa ke yi sa’i da lokaci.

Akwai dama-dama a fannin tsadar abinci da kuma karfin tattalin arziki, yayin da ake da zaman lafiya mai inganci idan aka kwatanta da sauran sassan duniya.

Bisa al’ada dai al’ummar musulmi kan kwashe tsahon kwanaki 29 ko kuma 30 suna azumtar watan na Ramadan da ke da matukar muhimanci a gare  su, yayin da yake cikin manyan ginshikan da ke rike da adddinin.

Muslim devotees offer a special morning prayer to start the Eid al-Fitr festival, which marks the end of their holy fasting month of Ramadan, at the Jama Masjid mosque in the old quarters of New Delhi on May 3, 2022. (Photo by Jewel SAMAD / AFP)

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara