Connect with us

Kasuwanci

Uwargidan Shugaban Kasa Ta Ba Matan Arewa Ta Gabas Su Dubu Tallafin Naira Miliyan 50

Published

on

Sanata Oluremi Tinubu yt gana da sarakunan Taraba, ta kuma ba da gudummawar naira miliyan 50 don tallafa wa mata 1,000, da kayan aiki dubu 10,000 ga ma’aikatan lafiya

 

Uwargidan shugaban Najeriya, Sanata Oluremi Bola Ahmed Tinubu, ta bukaci shugabannin gargajiya da su marawa shirin ta na sabon fata ta hanyar wayar da kan jama’a game da shirye-shiryen kiwon lafiya da ke gudana a fadin kasar.

 

Misis Tinubu ta yi wannan roko ne a Jalingo, babban birnin jihar Taraba, yayin wata ganawa da sarakunan gargajiya a ranar Alhamis, wanda aka gudanar a dakin taro na uwargidan gwamnan jihar.

 

Uwargidan shugaban kasa, Sen. Oluremi Bola Ahmed Tinubu da ta isa filin jirgin saman Danbaba Suntai a ranar Alhamis da tsakar rana, ta samu tarba daga gwamna Agbu Kefas da matarsa, Misis Agyin Kefas tare da manyan jami’an gwamnati, da kuma dimbin magoya bayan jam’iyyar PDP mai mulki a jihar da kuma babbar jam’iyyar adawa ta APC.

 

Mrs Tinubu ta kai ziyarar aiki ta kwanaki biyu a jihar Taraba, tare da rakiyar uwargidan mataimakin shugaban kasa, Hajiya Nana Kashim Shettima, ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Muhammed Ali Pate, da babban daraktan hukumar kula da lafiya matakin farko na kasa Dr Muyi Aina da dai sauransu.

 

Ziyarar ta na kuma da nufin karfafa gwiwar ma’aikatan kiwon lafiya na sahun gaba ta hanyar ba da tallafi da kuma sanin irin kokarin da suke yi, da kuma wayar da kan jama’a game da cutar kanjamau, musamman yaduwar cutar kanjamau daga uwa zuwa ’ya’ya.

 

Da take jawabi a yayin ganawarta da shugabannin gargajiya, Sen. Oluremi Tinubu, ta bayyana cewa hada kai da sarakunan gargajiya zai taimaka wa gwamnatin tarayya wajen isar da sako game da samarwa da kuma maganin cutar kanjamau da tarin fuka kyauta, inda ta bayyana muhimmiyar rawar da suke takawa wajen hada kan jama’a.

 

Da yake mayar da jawabi, Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Taraba kuma Aku Uka na Wukari, HRM Manu Ishaku Adda Ali, ya bayyana ziyarar Misis Tinubu a matsayin alheri ga jihar.

 

Sai dai Sanata Oluremi Tinubu, jim kadan bayan ganawarta da shugabannin gargajiya, ta zarce zuwa filin wasa na Jolly Nyame, inda ta kaddamar da rabon kayayyakin sana’o’in ga ungozoma a fadin yankin Arewa maso Gabas.

 

A nata jawabin, ta kuma jaddada kudirin gwamnatin tarayya na samar da ayyukan kiwon lafiya da nufin rage mace-macen mata da kananan yara a fadin kasar nan.

 

A nasa jawabin, Ministan Lafiya, Farfesa Ali Pate, ya ce a yankin Arewa maso Gabas kadai, an horar da ma’aikatan kiwon lafiya 8,500, daga cikinsu 1,300 daga jihar Taraba.

 

A cewarsa, sama da cibiyoyin kiwon lafiya 1,000 ne ke samun tallafi a duk shekara daga asusun samar da kiwon lafiyai, ciki har da 170 a jihar.

 

Gwamna Agbu Kefas ya yabawa uwargidan shugaban kasar bisa wannan karimcin, inda ya ce jihar ta yi tarayya cikin hangen nesa na shirin sabunta fata.

 

A nata bangaren, uwargidan gwamnan, Misis Agyin Kefas, ita ma ta nuna jin dadin ta bisa yadda aka yi musu dauki, sannan ta yabawa ministan lafiya da walwalar jama’a bisa jajircewar sa.

 

A halin da ake ciki, Sanata Oluremi Tinubu ya mika kayan sana’o’in hannu guda 10,000 ga ungozoma a fadin jihohin Arewa maso Gabas shida, sannan ta mika chekin kudi naira miliyan 50 domin tallafa wa mata 1,000 a jihar Taraba.

 

 

Sani Sulaiman

Labarai

Labarai3 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai23 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara