Connect with us

Labarai

Uwargidan Shugaban Kasa Remi Tinubu Ta Kaddamar Da Gasar Muhalli Ta Miliyoyin Kudi

Published

on

Uwargidan Shugaban Kasa Sanata Oluremi Tinubu, ta ƙaddamar wata gasa ta muhalli a faɗin ƙasa wacce aka ƙirƙira domin ƙarfafa dasa bishiyoyi, tsaftar muhalli da kuma rayuwa mai ɗorewa a Nijeriya, a karkashin Shirin Ayyukan Jin Kai da Cigaban Al’umma (RHI).

A yayin ƙaddamar da shirin a taron da take yi bayan watanni 3 da matan gwamnoni, wanda aka yi tare da shugabannin RHI na jihohi, Sanata Tinubu ta bayyana gasar a matsayin kira ga iyalai, ƙungiyoyin matasa, al’ummomi da gwamnatocin jihohi da su haɗa hannu wajen gina Nijeriya.

Gasar wacce aka yi wa taken “A Inganta Yau Domin Gobe Ta Yi Kyau” ta kasu kashi uku, wacce kowannensu ke da lada mai tsoka:

Gasa ta farko ita ce ta Iyali, wacce aka fi maida hankali kan jihohin Arewa 11 da sahara ta fi shafa, inda ake karfafa  kowane iyali su dasa aƙalla bishiya ɗaya, kuma wanda suka yi nasara za su karɓi kyautar Naira miliyan 20.

Haka kuma akwai rukuni na Al’umma wanda aka buɗe wa makarantu, ƙungiyoyin matasa, kungiyoyi masu zaman kansu da kuma kananan hukumomi a faɗin ƙasa domin farfaɗo da wuraren da aka lalata, ta hanyar mai da su lambuna, filayen shakatawa ko wuraren muhalli. Wadanda suka yi nasara a wannan rukuni na  kyautar Naira miliyan 50.

Rukuni da karshe kuma na jihohi ne, amma banda Jihar Enugu, inda su kuma  ake bukatar mai da  hankali kan dasa bishiyoyi a tituna da manyan hanyoyi, wanda Jihar da ta fi nuna kulawa wajen kare muhalli za ta samu Naira miliyan 100.

A wajen taron, Uwargidan Shugaban Kasar ta miƙa takardar ceki na Naira miliyan 100 ga Jihar Enugu wacce aka zaɓa a matsayin “Jihar da ta yi fice a yawan bishiyoyi” saboda jajircewarta wajen dasa bishiyoyi da kuma tsaftar muhalli.

Enugu ta cancanci wannan,” in ji Sanata Remi Tinubu. “Ba wai kawai dasa bishiyoyi take ba, har da tsaftace muhalli. Idan ka shiga Enugu, kana ganin tsafta, wanda hakan abin a yaba ne matuka.”

A matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin RHI, ta bayyana cewa suna aiki tare da Ma’aikatar Muhalli ta Ƙasa domin kafa kulob kulob na muhalli  a makarantun sakandare da manyan makarantu, domin ɗora matasa kan sanin muhalli da kare shi.

An tsara gasar RHI Green Nigeria Challenge  har zuwa shekara ta 2026, inda aka riga aka kafa wa’adin tura ayyuka. Ana kuma ƙarfafa masu sha’awar shiga gasar da su samu ƙarin bayani kuma su tura ayyukansu ta manhajar shirin wato www.hrinitiative.org.

 

Daga Bello Wakili  

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara