Labarai
Uwargidan Shugaban Kasa Remi Tinubu Ta Kaddamar Da Gasar Muhalli Ta Miliyoyin Kudi
Uwargidan Shugaban Kasa Sanata Oluremi Tinubu, ta ƙaddamar wata gasa ta muhalli a faɗin ƙasa wacce aka ƙirƙira domin ƙarfafa dasa bishiyoyi, tsaftar muhalli da kuma rayuwa mai ɗorewa a Nijeriya, a karkashin Shirin Ayyukan Jin Kai da Cigaban Al’umma (RHI).
A yayin ƙaddamar da shirin a taron da take yi bayan watanni 3 da matan gwamnoni, wanda aka yi tare da shugabannin RHI na jihohi, Sanata Tinubu ta bayyana gasar a matsayin kira ga iyalai, ƙungiyoyin matasa, al’ummomi da gwamnatocin jihohi da su haɗa hannu wajen gina Nijeriya.
Gasar wacce aka yi wa taken “A Inganta Yau Domin Gobe Ta Yi Kyau” ta kasu kashi uku, wacce kowannensu ke da lada mai tsoka:
Gasa ta farko ita ce ta Iyali, wacce aka fi maida hankali kan jihohin Arewa 11 da sahara ta fi shafa, inda ake karfafa kowane iyali su dasa aƙalla bishiya ɗaya, kuma wanda suka yi nasara za su karɓi kyautar Naira miliyan 20.
Haka kuma akwai rukuni na Al’umma wanda aka buɗe wa makarantu, ƙungiyoyin matasa, kungiyoyi masu zaman kansu da kuma kananan hukumomi a faɗin ƙasa domin farfaɗo da wuraren da aka lalata, ta hanyar mai da su lambuna, filayen shakatawa ko wuraren muhalli. Wadanda suka yi nasara a wannan rukuni na kyautar Naira miliyan 50.
Rukuni da karshe kuma na jihohi ne, amma banda Jihar Enugu, inda su kuma ake bukatar mai da hankali kan dasa bishiyoyi a tituna da manyan hanyoyi, wanda Jihar da ta fi nuna kulawa wajen kare muhalli za ta samu Naira miliyan 100.
A wajen taron, Uwargidan Shugaban Kasar ta miƙa takardar ceki na Naira miliyan 100 ga Jihar Enugu wacce aka zaɓa a matsayin “Jihar da ta yi fice a yawan bishiyoyi” saboda jajircewarta wajen dasa bishiyoyi da kuma tsaftar muhalli.
“Enugu ta cancanci wannan,” in ji Sanata Remi Tinubu. “Ba wai kawai dasa bishiyoyi take ba, har da tsaftace muhalli. Idan ka shiga Enugu, kana ganin tsafta, wanda hakan abin a yaba ne matuka.”
A matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin RHI, ta bayyana cewa suna aiki tare da Ma’aikatar Muhalli ta Ƙasa domin kafa kulob kulob na muhalli a makarantun sakandare da manyan makarantu, domin ɗora matasa kan sanin muhalli da kare shi.
An tsara gasar RHI Green Nigeria Challenge har zuwa shekara ta 2026, inda aka riga aka kafa wa’adin tura ayyuka. Ana kuma ƙarfafa masu sha’awar shiga gasar da su samu ƙarin bayani kuma su tura ayyukansu ta manhajar shirin wato www.hrinitiative.org.
Daga Bello Wakili
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
