Labarai
Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan
Daga Aminu Dalhatu
Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa kokarinsu na hadin gwiwa wajen samun nasarar rabon kayan abinci na watan Ramadan a kananan hukumomi 14 na jihar, domin tallafa wa marasa galihu da marayu.
Ta yi wannan yabon ne a lokacin rabon kayan a karamar hukumar Gusau, inda ta bayyana cewa an tsara shirin ne domin rage radadin rayuwa ga iyalai a wannan wata mai alfarma na Ramadan.

A cewarta, rabon ya shafi dukkan kananan hukumomin jihar, inda aka fara daga Shinkafi da Zurmi, sannan Birnin Magaji da Kaura Namoda, daga nan sai Gummi da Bukkuyum, Anka da Talata Mafara, Maradun da Bakura, Maru da Bungudu, sannan aka kammala a Tsafe da Gusau.
Hajiya Huriyya ta bayyana cewa an samu nasarar raba kunshin kayan abinci guda 50,000 a fadin jihar. Ta ce kowane kashi ya kunshi buhun shinkafa mai nauyin kilo 20, wake, masara da gero, da kilo 5 na sukari, taliya, man girki, gishiri, da kuma sutura ga mata.

Uwargidan gwamnan ta kuma bayyana cewa an kafa kwamitoci a matakin gunduma domin yin aiki tare da shugabannin kananan hukumomi, don tabbatar da adalci, gaskiya da rikon amana wajen rabon kayan.
“Mun umurci kwamitocin da su gudanar da aikinsu da gaskiya, rikon amana da tsoron Allah, domin sauje amanar da aka dora musu ce,” in ji ta.

Ta kuma gode wa mambobin tawagarta da suka hada da direbobi, jami’an tsaro, daraktocin Zakka da ma’aikatansu, ‘yan jarida, masu aikin sa kai da duk wadanda suka bada gudunmawa wajen samun nasarar shirin.
“Kun nuna jajircewa da sadaukarwa. Allah ne kadai zai saka wa kowa.” in ji ta.

Hajiya Huriyya ta kuma yaba wa Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, bisa goyon bayansa da jajircewarsa wajen inganta jin dadin al’ummar jihar, tare da sauran masu taimako da suka taka muhimmiyar rawa wajen nasarar shirin.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
