Labarai
Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan
Daga Aminu Dalhatu
Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa kokarinsu na hadin gwiwa wajen samun nasarar rabon kayan abinci na watan Ramadan a kananan hukumomi 14 na jihar, domin tallafa wa marasa galihu da marayu.
Ta yi wannan yabon ne a lokacin rabon kayan a karamar hukumar Gusau, inda ta bayyana cewa an tsara shirin ne domin rage radadin rayuwa ga iyalai a wannan wata mai alfarma na Ramadan.

A cewarta, rabon ya shafi dukkan kananan hukumomin jihar, inda aka fara daga Shinkafi da Zurmi, sannan Birnin Magaji da Kaura Namoda, daga nan sai Gummi da Bukkuyum, Anka da Talata Mafara, Maradun da Bakura, Maru da Bungudu, sannan aka kammala a Tsafe da Gusau.
Hajiya Huriyya ta bayyana cewa an samu nasarar raba kunshin kayan abinci guda 50,000 a fadin jihar. Ta ce kowane kashi ya kunshi buhun shinkafa mai nauyin kilo 20, wake, masara da gero, da kilo 5 na sukari, taliya, man girki, gishiri, da kuma sutura ga mata.

Uwargidan gwamnan ta kuma bayyana cewa an kafa kwamitoci a matakin gunduma domin yin aiki tare da shugabannin kananan hukumomi, don tabbatar da adalci, gaskiya da rikon amana wajen rabon kayan.
“Mun umurci kwamitocin da su gudanar da aikinsu da gaskiya, rikon amana da tsoron Allah, domin sauje amanar da aka dora musu ce,” in ji ta.

Ta kuma gode wa mambobin tawagarta da suka hada da direbobi, jami’an tsaro, daraktocin Zakka da ma’aikatansu, ‘yan jarida, masu aikin sa kai da duk wadanda suka bada gudunmawa wajen samun nasarar shirin.
“Kun nuna jajircewa da sadaukarwa. Allah ne kadai zai saka wa kowa.” in ji ta.

Hajiya Huriyya ta kuma yaba wa Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, bisa goyon bayansa da jajircewarsa wajen inganta jin dadin al’ummar jihar, tare da sauran masu taimako da suka taka muhimmiyar rawa wajen nasarar shirin.
-
Labarai3 days agoAdalci a Kauru LGA Yayin da Tsarin Raba Mukamai ke Kara Karɓuwa Domin Wakilci Nagari
-
Labarai5 days agoHukumar Alhazan Jihar Jigawa ta Kaddamar da Kwamitin Amirul Hajjin Bana
-
Labarai2 days agoRadio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya
-
Labarai7 days agoTrump Ya Aike da Daftarin Shirin Zaman Lafiya ga Iran
-
Labarai2 days agoMasarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin
-
Labarai2 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana
-
Labarai5 days agoHajjin2026: Jigawa ta Kara Kaimi Wajen Horar Da Maniyyata
-
Labarai2 days agoƊaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano
