Connect with us

Ilimi

Uwargidan Gwamnan Jihar Kwara Ta Bukaci Dalibai Su Kauracewa Shaye-shaye

Published

on

Uwargidan gwamnan jihar Kwara, Ambasada Olufolake AbdulRazaq, ta shawarci dalibai da su guji shaye-shayen miyagun kwayoyi, tare da gujewa dukkan wani nau’in tu’ammali da kwaya.

Uwargidan gwamnan ta bayar da wannan shawarar ce a makarantar sakandiren Sarauniya Elizabeth da ke Ilorin a yayin wani taron da kwamitin yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi na jihar Kwara da hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA) da ofishin uwargidan gwamnan jihar suka shirya, domin  wayar da kan dalibai a jihar, a bikin ranar yaki da tu’ammali da miyagun kwayoyi ta duniya da Majalisar Dinkin Duniya ta ayyana.

Uwargidan gwamnan wadda kwamishinar lafiya ta jihar Dr Amina Ahmed El-Imam ta wakilta,
ta jaddada mahimmancin dalibai su zama jakadu nagari ta hanyar gujewa miyagun kwayoyi da sauran abubuwan da ba su dace ba.

Ta kuma yi kira ga daliban Makarantu da su wayar da kan sauran daliban game da illolin shaye-shayen miyagun kwayoyi da gujewa cin zarafi ko yaudarar su da shan miyagun kwayoyi.

Uwargidan gwamnan, ta bayyana irin jajircewar da gwamnatin jihar ta yi na ganin  ta kawar da tu’ammali da miyagun kwayoyi a tsakanin dalibai.

Ta kuma bukaci daliban da su bai wa ilimi fifiko, inda ta kara da cewa ilimi shi ne abu mafi daraja da za su samu.

Ambasada  Olufolake AbdulRazq ta kara karfafawa daliban kwarin guiwa da su mai da hankali kan karatunsu tare da kaurace wa duk wani abu da zai illata rayuwarsu.

 

Ali Muhammad Rabi’u

Labarai

Labarai1 day ago

Ziyarar Shugaba Tinubu Zuwa China Ta Yi Nasara

  Ziyarar Shugaba Tinubu zuwa China Ta Yi Nasara, da kuma Shaida Wa ‘Yan Najeriya Mazauna China, Yi Alkawarin don...

Labarai2 days ago

Sabon Tsarin Albashi: Majalisar Kano Ta Amince da Karin Kasafin Naira Biliyan 99

Majalisar Dokokin Kano ta amince da ƙarin kasafin kudi na N99bn da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya aike mata domin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Zamfara Ta Musanta Jita-Jitar Bayar Da Kudi Ga ‘Yan Ta’adda

  Gwamnatin Jihar Zamfara tayi watsi da jita-jitar da ke yawo cewar tana shirin bayar da kudi ga wasu sanannun...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Dauki Matakan Gaggawa Don Wadata Man Fetur da Farashinsa

  Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Ɗauki Matakai Masu Ƙarfi don Magance Samuwar Man Fetur da Farashi a Faɗin Najeriya A...

Labarai2 days ago

Tinubu Ya Nemi Hadin Gwiwar Afirka da China Don Bunkasa Tattalin Arziki

  Shugaba Bola Tinubu ya yi kira da a ci gaba da hadin kai tsakanin Afrika da Sin, yana mai...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya ta Amince da Tsare-tsare Don Yakar Rashin Abinci Mai Gina Jiki

  Daga: Bello Wakili Ministan Tsare-tsare na Lafiya da Walwala ta Jama’a na kasa, Muhammad Ali Pate, ya jaddada muhimmancin...

Labarai3 days ago

ACF Ta Ce Babban Kalubalen Arewa Yanzu Shi Ne Rashin Tsaro

Kungiyar Tuntubar Arewa, wato Arewa Consultative Forum (ACF) ta ce a halin yanzu, batun da ya fi damun al’ummar arewacin...

Labarai3 days ago

Hukumar NOA Ta Yabawa Majalisar Jihar Nasarawa Wajen Samarda Dokoki Masu Amfani ga Jama’a

Hukumar Wayar da Kan Jama’a da Fadakarwa ta Kasa (NOA) ta yaba wa Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa bisa ga kafa...

Kasuwanci4 days ago

Shugaba Tinubu Ya Gana da Firayim Ministan Sin, Ya Ce Afirka Na Da Damar Zuba Jari da Haɓaka

  Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya ce Afrika na da manyan damammaki wajen zuba jari, ci gaba, da haɓaka tare...

Labarai4 days ago

Tinubu Ya Jajantawa Jihar Yobe Kan Rashe-Rashen Rayukan da Aka Yi a Tarmuwa

  Shugaba Bola Tinubu ya jajantawa gwamnati da al’ummar jihar Yobe kan rashin rayukan da aka yi a Mafa a...

Mafi Shahara