Connect with us

Ilimi

Uwargidan Gwamnan Jihar Kwara Ta Bukaci Dalibai Su Kauracewa Shaye-shaye

Published

on

Uwargidan gwamnan jihar Kwara, Ambasada Olufolake AbdulRazaq, ta shawarci dalibai da su guji shaye-shayen miyagun kwayoyi, tare da gujewa dukkan wani nau’in tu’ammali da kwaya.

Uwargidan gwamnan ta bayar da wannan shawarar ce a makarantar sakandiren Sarauniya Elizabeth da ke Ilorin a yayin wani taron da kwamitin yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi na jihar Kwara da hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA) da ofishin uwargidan gwamnan jihar suka shirya, domin  wayar da kan dalibai a jihar, a bikin ranar yaki da tu’ammali da miyagun kwayoyi ta duniya da Majalisar Dinkin Duniya ta ayyana.

Uwargidan gwamnan wadda kwamishinar lafiya ta jihar Dr Amina Ahmed El-Imam ta wakilta,
ta jaddada mahimmancin dalibai su zama jakadu nagari ta hanyar gujewa miyagun kwayoyi da sauran abubuwan da ba su dace ba.

Ta kuma yi kira ga daliban Makarantu da su wayar da kan sauran daliban game da illolin shaye-shayen miyagun kwayoyi da gujewa cin zarafi ko yaudarar su da shan miyagun kwayoyi.

Uwargidan gwamnan, ta bayyana irin jajircewar da gwamnatin jihar ta yi na ganin  ta kawar da tu’ammali da miyagun kwayoyi a tsakanin dalibai.

Ta kuma bukaci daliban da su bai wa ilimi fifiko, inda ta kara da cewa ilimi shi ne abu mafi daraja da za su samu.

Ambasada  Olufolake AbdulRazq ta kara karfafawa daliban kwarin guiwa da su mai da hankali kan karatunsu tare da kaurace wa duk wani abu da zai illata rayuwarsu.

 

Ali Muhammad Rabi’u

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara