Ilimi
Uwargidan Gwamnan Jihar Kwara Ta Bukaci Dalibai Su Kauracewa Shaye-shaye
Uwargidan gwamnan jihar Kwara, Ambasada Olufolake AbdulRazaq, ta shawarci dalibai da su guji shaye-shayen miyagun kwayoyi, tare da gujewa dukkan wani nau’in tu’ammali da kwaya.
Uwargidan gwamnan ta bayar da wannan shawarar ce a makarantar sakandiren Sarauniya Elizabeth da ke Ilorin a yayin wani taron da kwamitin yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi na jihar Kwara da hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA) da ofishin uwargidan gwamnan jihar suka shirya, domin wayar da kan dalibai a jihar, a bikin ranar yaki da tu’ammali da miyagun kwayoyi ta duniya da Majalisar Dinkin Duniya ta ayyana.
Uwargidan gwamnan wadda kwamishinar lafiya ta jihar Dr Amina Ahmed El-Imam ta wakilta,
ta jaddada mahimmancin dalibai su zama jakadu nagari ta hanyar gujewa miyagun kwayoyi da sauran abubuwan da ba su dace ba.

Ta kuma yi kira ga daliban Makarantu da su wayar da kan sauran daliban game da illolin shaye-shayen miyagun kwayoyi da gujewa cin zarafi ko yaudarar su da shan miyagun kwayoyi.
Uwargidan gwamnan, ta bayyana irin jajircewar da gwamnatin jihar ta yi na ganin ta kawar da tu’ammali da miyagun kwayoyi a tsakanin dalibai.
Ta kuma bukaci daliban da su bai wa ilimi fifiko, inda ta kara da cewa ilimi shi ne abu mafi daraja da za su samu.
Ambasada Olufolake AbdulRazq ta kara karfafawa daliban kwarin guiwa da su mai da hankali kan karatunsu tare da kaurace wa duk wani abu da zai illata rayuwarsu.
Ali Muhammad Rabi’u
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
