Connect with us

Labarai

Tsaftar Muhalli: An Bukaci Shugabannin Su Yi Koyi da Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

An bayyana rashin tsaftar muhalli a matsayin babbar hanyar haddasa matsalolin lafiya a cikin al’umma.

Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu, Dokta Builder Muhammad Uba, ya bayyana hakan a yayin aikin tsaftar muhalli na kowane wata da aka gudanar a Birnin Kudu.

Shugaban ya sake jaddada jajircewarsa wajen tabbatar da tsaftar muhalli ta hanyar halartar aikin tsaftar muhalli na karshen wata, wanda ake gudanarwa a duk ranar Asabar ta karshe ta kowane wata.

Dokta Muhammad Uba, ya jaddada muhimmancin tsaftar muhalli tare da kira ga al’ummar yankin da su rika tsaftace muhallinsu a kowane lokaci.

Ya bayyana cewa kula da tsaftar muhalli hakki ne da ya rataya a wuyan kowa da kowa domin samar da muhalli mai tsafta da lafiya.

Haka kuma, ya tabbatar wa al’umma cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da ba da goyon baya ga shirye-shiryen da ke inganta tsaftar muhalli da kula da lafiyar jama’a.

Builder ya kuma bukaci mazauna yankin da su dauki alhakin kula da muhallinsu tare da yin aiki tukuru domin tsaftace Karamar Hukumar ta Birnin Kudu.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa an gudanar da atisayen tsaftar muhalli na kowane wata a wuraren taruwar jama’a, kasuwanni da unguwanni, inda mahalarta suka bukaci masu ruwa da tsaki su yi koyi da kyakkyawan jagorancin Shugaban Karamar Hukumar tare da ba da fifiko ga tsaftar muhalli.

 

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara