Kasuwanci
Tinubu Yayi Sabbin Nade-Nade A Kasuwar Shinko Ta Kasa

Shugaba Bola Tinubu ya amince da nadin Mista Mairiga Aliyu Katuka a matsayin shugaban Hukumar kula da kasuwannin shinko na kasa.
Wata sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya fitar ta ce shugaban ya kuma nada Mista Emomotimi Agama a matsayin babban Darakta hukumar.
Frana Chukwuogor kuma an nada shi a matsayin Babban Kwamishinan kula da harkokin Shari’a.
Sai kuma Mista Bola Ajomale a matsayin Babban Kwamishinan kula da Ayyuka. Ita kuma Mrs. Samiya Hassan Usman a matsayin kwamishinar kula da harkokin hukumar.
Mista Lekan Belo kuwa a matsayin kwamishinan zartarwa. Da kuma Kasimu Garba Kurfi a matsayin Kwamishina.
Sanarwar ta kara da cewa, shugaba Tinibu ya bayyana kwarin gwiwar cewa dukkan mambobin hukumar za su yi amfani da kwarewarsu wajen ci gaba da aikin hukumar na samar da ingantacciyar kasuwa mai inganci, da gaskiya, ta yadda masu zuba jari za su samu kwarin gwiwa tare da bayar da gudummawa sosai ga harkokin kasuwanci. ci gaban tattalin arzikin kasa.
Bello Wakili/Wababe
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
