Labarai
Shugaba Tinubu Ya Taka Rawar Gani Sosai — Buhari

Tsohon Shugaban Kasa, Muhammadu Buhari, ya ce magajinsa, Bola Ahmed Tinubu, yana taka rawar gani sosai tun bayan hawansa mulki watanni tara da suka wuce.
Tsohon shugaban kasar, ya ce Tinubu ya taka rawar gani idan aka yi la’akari da yanayin da ake ciki, amma ya ce Najeriya kasa ce mai wuyar sha’ani.
Buhari ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin shugaban Hukumar Kwastam, Bashir Adewale Adeniyi da wasu jami’an hukumar a Daura a ranar Lahadi.
Tinubu dai ya fuskanci suka kan wasu daga cikin manufofin da ya bijiro da su game da tattalin arziki da suka hada da cire tallafin man fetur.
Buhari ya ce yana da matukar wahala ga ‘yan kasar su iya jure matsin tattalin arziki da ake fama da shi, sai dai ya ce yana goyon bayan manufofi da tsare-tsaren gwamnati mai ci.
“Na gode kwarai da ziyararku. Na yaba sosai. Ina kyautata zaton Tinubu ya yi kokari sosai zuwa yanzu,” in ji Buhari.
“Najeriya tana da sarkakiya sosai. Hakika, da wuya wani ya iya wani abun a zo a gani.”
Har wa yau, shugaban na Kwatsam ya ziyarci mai martaba Sarkin Daura, Dokta Farouk Umar Farouk.
A yayin ziyarar, Adeniyi ya ce “Wannan mataki na doka ya bai wa hukumar Kwastam damar fadada manufofin samar da kudaden shiga da kuma saukaka harkokin kasuwanci, haka kuma ya taimaka sosai ga ci gaban tattalin arzikin Najeriya,” in ji Adeniyi.
Idan dai ba a manta ba, wannan ba shi ne karon farko da Buhari ya yi furuci kan wahalar shugabanci da Najeriya ta ke da shi ga masu rike da akalar jagoranci ba.
“’Yan Najeriya na da wahala wajen shugabanci. Mutane ne da suka san hakkinsu. Suna ganin ya kamata su kasance a wajen ba kai ba. Don haka, suna lura da kusan kowane mataki da aka dauka. Kuma dole ne ka jajirce dare da rana don tabbatar da cewa ka yi kokari sosai,” in ji Buhari.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
