Ilimi
Sheikh Daurawa Ya Yi Murabus Daga Shugabancin Hisba

Shugaban Hukumar Hisba na Jihar Kano, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, ya yi murabus da mukaminsa.
Daurawa ya sanar da saukarsa daga shugabancin hukumar ne bayan kalaman gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf, ya yi na sukar yadda hukumar ke gudanar da ayyukanta na yaki da badala a jihar.
Daurawa, ya sanar da murabus dinsa daga shugabancin hukumar, a wani bidiyo da ya wallafa a shafinsa na Facebook da safiyar ranar Juma’a.
Kalaman gwamna Abba Gida-Gida, sun yamutsa hazo a jihar, inda wasu ke ganin kalaman nasa a matsayin wata gaba ta goyon bayan masu aikata badala a jihar.
Idan ba a manta ba hukumar Hisba a jihar ta fito da sabon salon yaki da baɗala, inda ta dinga kai samame wurare shakatawa da otal-otal tana kama masu yawon ta-zubar.
Daga bisani Murja ta yi layar bata daga gidan yari, lamarin da ya tayar da kura da haifar da cece-kuce musamman a kafafen sada zumunta.
Sai dai gwamnatin jihar a wani martani da ta yi, ta hannun Kwamishinan Yada Labaran jihar, Baba Dantiye, ya musanta wannan zargi da ake yi wa gwamnatin.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
