Connect with us

Labarai

Sarkin Musulmi Ya Ayyana Ranar Juma’a 1 ga Watan Shawwal

Published

on

Daga Nasir Malali

Mai Martaba Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar, ya ayyana ranar Juma’a, 20 ga watan Maris a matsayin ranar 1 ga Shawwal na shekarar 1447 bayan hijira, wanda hakan ke nuna ƙarshen azumin Ramadan na wannan shekara.

A cikin wata sanarwa da shugaban Kwamitin Shawarwari kan Harkokin Addini na Majalisar Masarautar Sakkwato, Sambo Wali Junaidu ya sanya wa hannu, ya bayyana cewa Majalisar Masarautar tare da Kwamitin Duba Wata na Ƙasa ba su samu wani rahoto da ke tabbatar da ganin jinjirin watan Shawwal ba a yau Laraba, 18 ga watan Maris na 2026, wanda ya yi daidai da 29 ga watan Ramadan na shekarar 1447 bayan hijira.

Sanarwar ta ƙara da cewa ranar Juma’a, 20 ga watan Maris, wadda ta yi daidai da 1 ga Shawwal, ita ce ranar gudanar da Sallar Idi da kuma bikin Eid-el-Fitr.

Mai Martaba Sarkin Musulmin ya taya al’ummar Musulmin Najeriya murna, tare da fatan alkairi.

Labarai

Labarai8 hours ago

Sarkin Musulmi Ya Ayyana Ranar Juma’a 1 ga Watan Shawwal

Daga Nasir Malali Mai Martaba Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar, ya ayyana ranar Juma’a, 20 ga watan Maris a matsayin...

Labarai2 days ago

Gidauniyar NASARA Ta Raba Kayayyakin Ramadan da na Sallah ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Marayu da zawarawa sama da dubu ɗaya ne suka amfana da tallafin kayayyakin Ramadana da na Sallah...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Taiwo Oyedele Ministan Kudi

Daga Bello Wakili  Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Taiwo Oyedele a matsayin  Minista a Ma’aikatar. An gudanar...

Labarai3 days ago

Yi Wa Shuwagabanni Biyayya Ne Zai Kai mu Ga Ci Gaba – Garkuwan Kudun Zazzau

Dokta Muhammad Sani Uwaisu FCNA, Garkuwan Kudun Zazzau, ya yi kira ga daukacin al’ummar Musulmin Duniya baki daya da su...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Zamfara Ta Amince da Biyan Albashin Watan Maris Gabanin Bukukuwan Karamar Sallah

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta amince da biyan albashin watan Maris da wuri ga dukkan ma’aikatan gwamnati da...

Labarai3 days ago

Mambobin APC Sun Kai 158,697 a Zamfara Bayan Sauya Shekar Gwamna Lawal

Adadin mambobin jam’iyyar APC a jihar Zamfara ya karu zuwa 158,697, kwanaki uku kacal bayan sake bude tsarin rajistar mambobi...

Labarai3 days ago

Kwara NUJ Iftar: An Bukaci ‘Yan Jarida Su Rika Tsayawa Kan Gaskiya

An bukaci ‘yan jarida su tabbatar rahotanninsu sun dogara da gaskiya tare da guje wa son zuciya domin kare mutuncinsu...

Labarai3 days ago

‘Yan Sanda Sun Bankado Maboyar Masu Garkuwa

Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta ce ta samu wani gagarumin nasara a kokarinta na yaki da masu garkuwa da...

Labarai3 days ago

JIBWIS Ta Bukaci Gwamna Bago Ya Gaggauta Sanya Hannu Kan Dokar Hisbah

Shugaban Majalisar Malamai ta ƙasa na ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS), Ash Sheikh Sani Yahaya Jingir, ya...

Labarai6 days ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Mafi Shahara