Connect with us

Labarai

Sanata Yari Ya Bada Gudummawar Kudi Ga Wadanda Harin Sama Ya Shafa A Maradun

Published

on

Tsohon Gwamnan Jihar Zamfara, Abdul’azeez Yari Abubakar, ya bayar da naira miliyan 23 da kuma buhuna 105 na kayan abinci ga wadanda lamarin harin sama da Rundunar Sojin Sama ta kasa ta kai a Karamar Hukumar Maradun, Jihar Zamfara ya shafa.

 

A cikin wata sanarwa da aka fitar wa manema labarai, Shugaban Kwamitin sadarwa na kungiyoyin siyasar tsohon gwamnan, Ibrahim Muhammad, ya bayyana cewa an bayar da wannan gudummawar ne a lokacin ziyarar ta’aziyya da aka kai ga Mai Martaba Sarkin Maradun, Alhaji Garba Muhammad Tambari, a fadarsa.

 

Alhaji Abdul’azeez Yari Abubakar, wanda shi ne Sanatan da ke wakiltar yankin Zamfara ta yamma a Majalisar Dattawa ta kasa, an wakilce shi ne ta hannun Kwamishinan Tarayya a Hukumar Kidaya ta Kasa a Jihar Zamfara, Alhaji Muhammad Muttaƙa Rini. Ya bayyana lamarin a matsayin nufin Allah.

 

Ya bukaci iyalan wadanda suka rasu da wadanda suka samu raunuka su dauki wannan lamarin a matsayin kaddara wanda ba zai yiwu a kauce masa ba.

 

Sanatan ya bayyana cewa, daga cikin shirye-shiryen agajin, kowanne iyali na wadanda suka rasu zai samu naira miliyan daya da buhuna biyar na abinci, yayin da wadanda suka ji rauni za su samu naira dubu dari biyar da buhuna biyu na abinci kowanne.

 

“Ya roki Allah SWT yai ma mutanen 13 da suka rasu sakamako da Aljannatul Firdausi, ya ba iyalansu da yankin Gidan Goga da Masarautar Maradun karfin hali don daukar wannan rashin da kuma saurin samun sauki ga wadanda suka ji rauni 20,” a cewar sanarwar.

 

Alhaji Abdul’azeez Yari Abubakar ya tabbatar wa da al’ummar Jihar Zamfara da dukkan yankin Arewa maso Yamma cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu na da niyyar dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a cikin jihar da kuma yankin baki daya.

 

A nasa bangaren, Mai Martaba Sarkin Maradun, Alhaji Garba Muhammad Tambari, ya yi godiya ga kyautar Sanatan, yana mai jaddada cewa wannan tallafin zai taimaka sosai wajen rage wahalar da wadanda abin ya shafa.

 

Sarkin ya bayyana matakin Sanata Abdulazeez Yari Abubakar a matsayin shaidar nuna martani mai kyau ga bukatun al’ummarsa a kowane lokaci.

 

Idan za a tuna, mafi yawan wadanda wannan mummunan lamari ya shafa sun fito ne daga kauyen Kakindawa na Karamar Hukumar Gidan Goga a Masarautar Maradun, Jihar Zamfara.

 

REL/AMINU DALHATU

Labarai

Labarai7 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara