Connect with us

Labarai

Sanata Barau Ya Kai Ziyarar Gani Da Ido Aikin Da Ake Yi A AKTH

Published

on

Gwamnatin Tarayya ta sake jaddada kudirinta na inganta harkar kiwon lafiya a fadin kasar nan, daidai da manufar sabunta kudiri na Shugaba Bola Ahmed Tinubu, wato Renewed Hope Agenda.

Wannan tabbacin ya fito ne daga Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, yayin da yake ziyarar duba ayyukan gine-gine da ke gudana a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH), wanda shi ne ya tallafa wajen samar da su.

Yayin da yake magana da ’yan jarida a lokacin ziyarar, Sanata Barau ya ce wadannan ayyuka na da nufin kara karfin cibiyoyin kiwon lafiya a cikin gida, tare da rage yawan tafiyar da ake yi zuwa kasashen waje domin neman magani, ta hanyar samar da ingantattun kayan aiki a asibitocin cikin gida.

Wadannan shirye-shirye suna cikin cikakkiyar manufa ta Shugaba Tinubu ta farfado da sashen kiwon lafiya,” in ji shi. “Nigeria na da kwararrun ma’aikatan lafiya, kuma idan aka samar musu da ingantattun kayan aiki, za a karfafa gwiwarsu, kuma za mu iya cimma burin kasa wajen ingantaccen tsarin kiwon lafiya.”

Dan majalisar ya kara da cewa, idan an kammala wadannan ayyuka, za su taimaka wajen kara ingancin ayyukan asibitin, tare da bai wa jama’a damar samun kulawar lafiya ta zamani da inganci.

A nasa bangaren, Babban Daraktan Asibitin, Farfesa Abdulrahman Sheshe, ya nuna godiya bisa wannan taimako, yana mai cewa ayyukan suna tafiya yadda ya kamata, kuma ana sa ran kammalawa da kaddamar da su kafin shekarar 2026.

A cewarsa, ayyukan sun hada da gina Cibiyar Nazarin Cutar Zuciya da Kwakwalwa (Cardio-Cerebral Center), Cibiyar Kula da Yara (Pediatric Center), da masaukan daliban jinya, da sauran muhimman gine-gine.

Wadannan sabbin cibiyoyi za su kara yawan gadon marasa lafiya, kuma za su ba mu damar gudanar da ayyukan da ba mu iya yi ba a baya,” in ji Farfesa Sheshe.

Ya kara da cewa, sabbin cibiyoyin za su kara ingancin ayyuka, tare da karfafa matsayin asibitin wajen zama jagora a harkar kiwon lafiya a yankin.

 

Abdullahi Jalaluddeen

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara