Connect with us

Labarai

Sabon Tsarin Sufuri Na BRT Zai Rage Kudin Sufuri Da Zirga-Zirga A Kaduna

Published

on

 

Hukumar Kula da Sufuri ta Jihar Kaduna tace shirin Bus Rapid Transit BRT da ake shirin kaddamarwa zai taimaka matuka wajen rage kudaden sufuri ga mazauna jihar, da zarar an fara aiwatar da shi.

 

Daraktan Hukumar, Injiniya Inuwa Ibrahim, ne ya bayyana hakan yayin wani taron tattaunawa da masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Kada Hive da ke Kaduna.

 

An shirya taron ne domin wayar da kan jama’a game da shirin BRT, sannan matakan da aka dauka ya zuwa yanzu.

 

Taron an gudanar da shi ne domin sauraron ra’ayoyin al’umma kan yadda za a aiwatar da shi cikin nasara.

 

Injiniya Inuwa ya bayyana cewa tsarin BRT zai taimaka wajen rage cunkoson ababen hawa da kara tsaro da aminci, da kuma inganta rayuwar al’umma baki daya a Jihar Kaduna.

 

Ya tuna cewa kimanin watanni biyu da suka gabata ne Gwamna Uba Sani ya kaddamar da sama da motoci 100 masu amfani da iskar gas na CNG, wadanda za su rika zirga-zirga a cikin Birnin Kaduna, Zariya da Kafanchan, a wani bangare na kokarin gyara tsarin sufuri a fadin jihar.

 

Ya bukaci mahalarta taron su yada ilimin da suka samu zuwa cikin al’ummominsu domin kara fahimta da goyon bayan jama’a don nasarar wannan shiri.

 

A nasa bangaren, Ted Regino, shugaban Rebel Artic Joint Venture, wanda ke sa ido kan kwangilolin aikin, ya ce kamfaninsa ne ke lura da yadda ake gudanar da aikin.

 

Ya tabbatar da cewa za a kammala aikin BRT kafin shekarar 2027, tare da karin bayani cewa kamfaninsu ya taba aiwatar da manyan ayyuka a kasa da kasa, kuma hakan zai maimaitu a Jihar Kaduna.

 

A nata jawabin, Shugabar Jam’iyyar Matan Arewa, Hajiya Rabi Saulawa, ta yaba da wannan shiri, tana mai cewa zai rage wa mata wahalhalun sufuri, musamman wadanda ke yawan zirga-zirga zuwa asibitoci, kasuwanni, wuraren aiki da makarantu.

 

Wasu daga cikin mahalarta sun jaddada bukatar kulawa da kiyaye motocin, tabbatar da dorewar shirin, da kuma kawo karshen matsalar sayar da tikiti ba bisa ka’ida ba.

 

Taron ya samu halartar wakilai daga sashen sufuri, shugabannin addinai da na gargajiya, ’yan jarida da sauransu.

 

COV: Adamu Yusuf

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara