Connect with us

Labarai

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Published

on

Daga Sani Dutsinma

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kebbi bayan duba kayayyakin aiki da shirye-shiryen da aka tanada domin gudanar da aikin Hajji cikin nasara.

Shugaban tawagar binciken, Injiniya Abba Shu’aibu Babagana ne ya bayyana hakan yayin ziyarar aiki da ya jagoranta zuwa jihar ta Kebbi.

A yayin ziyarar, jami’an NCAA sun duba muhimman wurare da dama a sansanin Alhazai na Kauran Gwandu Hajj Camp domin tantance yadda aka shirya kafin fara jigilar maniyyata zuwa aikin Hajjin bana.

Sun kuma ziyarci Cibiyar ICT, inda ake gudanar da rajista da sarrafa bayanan maniyyata ta hanyar fasahar zamani.

Hakazalika, tawagar ta duba Dakin Taro da ake amfani da shi wajen gudanar da tarurruka, da kuma Dakin Tantancewa  inda ake  gwajin lafiya, tabbatar da takardu, da sauran matakan tantancewa domin tabbatar da ganin dukkan maniyyata sun cika ka’idojin tafiya kafin a tafi aikin Hajji.

Jami’an NCAA sun kuma zagaya harabar sansanin Alhazan gaba ɗaya, inda suka nuna gamsuwa da tsafta, tsari, da kuma kayayyakin da aka tanada domin tallafawa maniyyata yayin shirye-shiryen tafiya.

A cewar jami’an, kayayyakin more rayuwa da tsare-tsaren da Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kebbi ta samar, na nuna irin ƙoƙarin gwamnatin jihar wajen tabbatar da cewa an gudanar da aikin Hajji cikin tsari, aminci, da inganci.

Ziyarar na daga cikin binciken da hukumar ke yi akai-akai domin tabbatar da cewa jihohi suna bin ƙa’idojin sufurin jiragen sama da ka’idojin aiki da ake buƙata domin nasarar jigilar maniyyata zuwa Saudi Arabia.

Labarai

Labarai2 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai1 day ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi1 day ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara