Connect with us

Labarai

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Published

on

Daga Sani Dutsinma

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kebbi bayan duba kayayyakin aiki da shirye-shiryen da aka tanada domin gudanar da aikin Hajji cikin nasara.

Shugaban tawagar binciken, Injiniya Abba Shu’aibu Babagana ne ya bayyana hakan yayin ziyarar aiki da ya jagoranta zuwa jihar ta Kebbi.

A yayin ziyarar, jami’an NCAA sun duba muhimman wurare da dama a sansanin Alhazai na Kauran Gwandu Hajj Camp domin tantance yadda aka shirya kafin fara jigilar maniyyata zuwa aikin Hajjin bana.

Sun kuma ziyarci Cibiyar ICT, inda ake gudanar da rajista da sarrafa bayanan maniyyata ta hanyar fasahar zamani.

Hakazalika, tawagar ta duba Dakin Taro da ake amfani da shi wajen gudanar da tarurruka, da kuma Dakin Tantancewa  inda ake  gwajin lafiya, tabbatar da takardu, da sauran matakan tantancewa domin tabbatar da ganin dukkan maniyyata sun cika ka’idojin tafiya kafin a tafi aikin Hajji.

Jami’an NCAA sun kuma zagaya harabar sansanin Alhazan gaba ɗaya, inda suka nuna gamsuwa da tsafta, tsari, da kuma kayayyakin da aka tanada domin tallafawa maniyyata yayin shirye-shiryen tafiya.

A cewar jami’an, kayayyakin more rayuwa da tsare-tsaren da Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kebbi ta samar, na nuna irin ƙoƙarin gwamnatin jihar wajen tabbatar da cewa an gudanar da aikin Hajji cikin tsari, aminci, da inganci.

Ziyarar na daga cikin binciken da hukumar ke yi akai-akai domin tabbatar da cewa jihohi suna bin ƙa’idojin sufurin jiragen sama da ka’idojin aiki da ake buƙata domin nasarar jigilar maniyyata zuwa Saudi Arabia.

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara