Fasaha
Najeriya Ta Karɓo Rancen Dala Biliyan 1.3 Don Kammala Layin Dogon Kano Zuwa Maraɗi

Gwamnatin Najeriya ta karɓo rancen dala biliyan 1.3 domin kammala aikin titin jirgin ƙasa daga Kano zuwa Maraɗi da ke Jamhuriyyar Nijar.
Bayanin hakan na kunshe ne cikin sanarwar da Ma’aikatar Sufuri ta Tarayya ta yi a ranar Laraba.
Sanarwar ta kuma bayyana cewa kamfanin gine-gine na ƙasar China, CCECC, ne zai samar da kaso 85 na kuɗaɗen da ake buƙata.
Haka kuma, ma’aikatar ta ce Gwamnatin Najeriya da haɗin gwiwar Bankin habaka tattalin arzikin Afirka na Africa Development Bank ne ke ɗaukar nauyin aikin.
“Samun bashin na dala biliyan 1.3 na nuna irin nasarar da za a samu wajen kammala layin dogon,” in ji sanarwar.
Wannan dai na ɗaya daga cikin shirye-shiryen Gwamnatin Najeriya na inganta harkar sufuri a faɗin ƙasar domin bunkasa tattalin arziki da ke fama da masassara.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
